BBC News, Hausa - Labaran Duniya
Babban Labari
Zan mayar da tallafin man fetur idan na ci zaɓe - Atiku
Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 20 ga watan Agustan 2026.
Kalmomin Turanci 10 da aka Hausantar da su a shafukan sada zumunta
Masana harshen Hausa sun bayyana cewar irin wannan salo na Hausantar da kalmomi yana taƙaita rubutu sannan yana sa hira da yi sauri.
Shugaba Paul Biya na Kamaru ya koma gida bayan shafe watanni biyu a ƙetare
Shugaban Kamaru, Paul Biya ya koma ƙasarsa bayan shafe fiye da watanni biyu yana wani abin da aka bayyana a matsayin "zama na ƙashin kai" a birnin Geneva na ƙasar Switzerland.
Yadda za ku kauce wa kamuwa daga ciwon idon Apollo
Ciwon na haifar da damuwa musamman a wuraren taruwar jama'a kamar makarantu, kasuwanni da ofisoshi, inda mutane ke yawan mu'amala da juna.
Abu 4 da gwamnatin Najeriya ta ce ta yi da kuɗin tallafin man fetur da ta tara
A lokacin cire tallafin, Shugaba Tinubu ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon yadda ake zargin cewa wasu tsiraru na amfani da tallafin wajen arzurta kansu.
Jihohin Najeriya 5 da kowane ɗantakarar shugaban ƙasa ke son lashewa
Duk da cewa Tinubu tsohon gwamnan Jihar Legas ne, ya sha kaye a jihar a zaben 2023 a hannun Peter Obi, yayin da Atiku ya yi nasara a wasu muhimman jihohin Arewacin Najeriya.
Shin ko Iran da Amurka sun shiga wani sabon zangon yaƙi ne?
Ranar Litinin, 17 ga Agustan 2026, ta zama ƙarshen wa'adin kwanaki 60 da aka bai wa Iran da Amurka domin cimma wata yarjejeniya mai faɗi da za ta kawo ƙarshen yaƙin, ta kuma magance batun shirin nukiliyar Iran, tare da sake buɗe mashigar ruwa ta Hormuz.
Abubuwa 6 da INEC ta haramta game da yaƙin neman zaɓe
Yaƙin neman zaɓe, lokaci ne da aka fi samun rikici da musayar wayu tsakanin mabiya jam'iyyu daban-daban a Najeriya, inda a wasu lokutan ma ake sabun tashe-tashen hankula.
Yadda za ku fara kasuwanci da ƙaramin jari har ya bunƙasa
A Najeriya da ke fama da hauhawar farashin kayayyaki, ƙarancin kuɗi da kuma tsadar yanayin gudanar da sana'a ko kuma kasuwanci, farawa da ƙaramin jari na iya zama babban ƙalubale.
Shirye-shiryenmu
Saurari na gaba, Shirin Safe, 05:29, 21 Agusta 2026, Tsawon lokaci 30,00
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban na duniya.
Saurari, Shirin Yamma, 19:29, 20 Agusta 2026, Tsawon lokaci 30,00
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban-daban na duniya.
Saurari, Shirin Rana, 13:59, 20 Agusta 2026, Tsawon lokaci 30,00
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban-daban na duniya.
Saurari, Shirin Hantsi, 06:30, 20 Agusta 2026, Tsawon lokaci 29,30
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban na duniya.
Wasanni
KAI TSAYE, Bai kamata a bar Vinicius ya bar Real Madrid ba - Mourinho
Wannan shafi na kawo muku labaran wasanni ne daga sassan duniya, kasuwar musayar 'yan wasa da kuma manyan sauye-sauyen da ke faruwa a fagen
Man City da Man Utd na hamayya kan Kone, Barca ta haƙura da Alvarez
Manchester City na shirin hamayya da Manchester United kan Manu Kone, Aston Villa na son Tosin Adarabioyo yayin da Tottenham ke tattaunawa domin ɗauko ƴanwasan Man City guda biyu.
Harry Kane zai koma Al Hilal, Newcastle na zawarcin Nico Gonzalez
Al-Hilal na tattaunawa da Harry Kane da Ollie Watkins, Newcastle na nazari kan Nico Gonzalez yayin da ƙoƙarin Sunderland na mallakar Dayann Methalie ke neman rushewa.
Man City ta dage kan Enzo Fernandez, Sao Paulo da West Ham na neman Vardy
Manchester City ta dagae kan Enzo Fernandez, ƙungiyoyi na neman ɗanwasan gefen Chelsea, Pedro Neto, yayin da aka yi wa ɗanwasan tsakiyar Manchester United, Bruno Fernandes tayin albashi mai tsoka.
Barcelona da Atletico na rububin Ounahi, Juventus ta haƙura da Martinez
Juventus ta janye daga zawarcin Emiliano Martinez, Manchester City na fuskantar hamayya a cinikin Pedro Neto, yayin da Real Madrid ke fatan ɗaukar Martin Zubimendi.
Tashar WhatsApp ta BBC Hausa
A wannan shafin za ku samu labarai daga ƙasashen Afrika da kuma sauran sassan duniya da ɗumi-ɗuminsu domin masu bibiyar mu a WhatsApp.
Kuna son tattalin datarku?
Shiga shafinmu na labarai maras hoto domin rage zuƙar data
Labarai da Rahotanni Na Musamman
Me yarjejeniyar zaman lafiya da jam'iyyu suka sanya wa hannu ta ƙunsa?
A ranar Talatya ne manyan jam'iyyun siyasa da ƴan takararsu suka sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya (Peace Accord) a Abuja, inda suka yi alƙawarin gudanar da yaƙin neman zaɓen cikin lumana da mutunta dokokin zaɓe.
Waɗanne masarautu Ɗanfodio ya ci da yaƙi kuma ina ne ake kira daular Sokoto?
Masanin tarihin ya ce a yankin Gudu da ke jihar Sakkwato ne Shehu Usman Danfodiyo ya fara kafa tuta.
Me ya sa sanin inzalin mace ke da wuya?
Kama daga sanin ainahin wurin da mace ta fi jin daɗi a taɓa mata, da yin inzali fiye da sau ɗaya, sanin ilimin yadda jin daɗin jikin mace yake ta fannin jima'i abu ne da a da ya gagari masana kimiyya.
Jiragen yaƙi 6 da suka fi tsananin gudu da ƙasashen da suka mallake su
Tsawon lokaci, jirgin yaƙin Amurka na F-16 ya kasance ɗaya daga cikin jiragen yaƙi mafiya gudu a duniya.
Kun san shafe dogon lokaci cikin talauci na iya taɓa lafiyar ƙwaƙwalwarku?
Wani bincike da masana kimiyya na Birtaniya suka yi ya gano cewa mutanen da ke fuskantar matsalolin kuɗi na tsawon lokaci na da yiwuwar samun kansu cikin larurar ƙwaƙwalwa da raguwar ƙarfin tunani da sarrafa bayanai yayin da suka kai matsakaitan shekaru.
Abin da ya kamata ku sani kan yaƙin neman zaɓen Najeriya da za a fara yau
''Kamar yadda dokar zaɓe ta 2026 ta tanadar, sashe na 94, sakin layi na biyu, ya buƙaci jam'iyyun siyasa su fara yaƙin neman zaɓe na shugaban ƙasa da kuma 'yan majalisu na tarayya, kwanaki 150 kafin ranar zaɓe.''
Yadda dangin Adeleke suka mamaye siyasar jihar Osun
Iyalan Chief Raji Adeleke na daga cikin fitattun ƴan siyasar da suka daɗe suna tasiri a tarihin siyasar Najeriya, musamman a jihar Osun.
Yadda bidiyon IS ya nuna mayaƙan ƙasar waje a Najeriya
Akwai yiwuwar cewa Abu ishaq ɗin da sojojin Najeriya suka ambata shi ne Abu Ishaq al-Maqdisi, inda "al-Maqdisi" ke nuna cewa ɗan Falasdinu - wanda aka gani a wani bidiyon ISWAP na watan Disamban 2024.
UAE ta sanar da dakatar da duk wata hulɗar kasuwanci da Iran
Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 16 ga watan Agustan 2026.
Mece ce makomar Jami'ar Jihar Kaduna bayan malamai fiye da 200 sun bar ta?
Dr Abdullahi ya ce malaman da suka bar jami'ar sun haɗa da manyan malamai, ciki har da farfesoshi, lamarin da ya bayyana a matsayin babbar barazana ga ingancin koyarwa da bincike da ci gaban jami'ar gaba ɗaya.
Dalilai 5 da suka sa gwamnan Osun Adeleke ke son tiƙar rawa
Ademola Adeleke, gwamnan jihar Osun a Najeriya, ya shahara da laƙabin "Dancing Governor" wato gwamna mai yawan rawa saboda yawan rawar da yake yi a wuraren taro da bukukuwa.
Mece ce manufar haɗakar tsaro tsakanin Turkiyya da Saudiyya da Pakistan?
An yi wa yarjejeniyar tsaron Turkiyya, Saudiyya da Pakistan lakabi da "NATO ta Musulmi". Amma shin hakan zai yi aiki a aikace?
KAI TSAYE - Labaran BBC Hausa
Saurari labaran BBC Hausa Kai Tsaye Litinin zuwa Juma’a da karfe 0530, 0630, 1400 da 1930 GMT, sai kuma Asabar da Lahadi da karfe 0530, 0630 da 1930 GMT.






























































