KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 29/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 29 ga watan Yunin 2026.

Taƙaitattu

Skip Bidiyo and continue reading
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Kutama
  • xxx
  • Sadis Buba

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Iran ta ƙara ƙaimi wajen yin kutse ta intanet tun bayan fara yaƙi - Isra'ila

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Babban jami’in tsaron intanet na Isra’ila ya ce Iran ta ƙara ƙaimi wajen yin kutse ta intanet tun bayan fara yaƙi tsakanin ƙasashen biyu.

    Yossi Karadi ya bayyana cewa an samu ƙaruwa a kutsen intanet daga Iran a cikin watannin baya-bayan nan.

    A wata hira da ya yi da jaridar Die Welt ta Jamus, Karadi ya ce a watan Yunin 2025, lokacin da Isra’ila ke gudanar da hare-haren soji kan Iran, sun gano kusan kutse ta intanet daga Iran 1,600.

    Amma a cikin makonni huɗu na baya-bayan nan na Yunin 2026, adadin ya ƙaru zuwa kusan 4,800.

    Ya ƙara da cewa masu yin kusten daga Iran ƙwararru ne sosai inda ya kuma ce dole ne a ɗauki lamarin da muhimmanci.

    Karadi ya kuma ce kutsen da Iran take yi ta intanet ɗin na harin muhimman cibiyoyin ƙasa, da ƙananan da matsakaitan kamfanoni kamar na lauyoyi da masu binciken kuɗi, da kuma jama’a baki ɗaya..

  2. Hare-haren saman Pakistan a Afghanistan sun hallaka mutane da dama

    Wani kakakin gwamnatin Taliban ya ce hare-haren sama da Pakistan ta kai kan yankuna a Afghanistan sun yi sanadiyyar kashe da jikkata fararen hula da dama, ciki har da mata da yara, a lardunan Paktika, Paktia da Kunar.

    Zabihullah Mujahid ya bayyana matakin na Pakistan a matsayin hari na “ban tsoro da ta’addanci,” yana mai cewa abin da ya faru ya saɓawa dokokin kasa da kasa ne.

    A wasu hotuna da aka wallafa a shafukan sada zumunta, an ga yara da fararen hula da suka jikkata sakamakon hare-haren.

    Sai dai a nata ɓangaren, Pakistan ta ce ta kai harin ne kan wuraren da ke karkashin mayaƙan Tehreek-e-Taliban Pakistan (TTP) da Jamaat-ul-Ahrar, inda ta ce ta kashe aƙalla mayaƙa 25.

    Jami’an Taliban sun ce aƙalla mutane 38 ne suka rasa rayukansu a hare-haren na daren jiya, inda mataimakin kakakin gwamnatin ya ƙara da cewa mutum 30 daga cikinsu sun mutu ne a kauyen Mandokhel da ke gundumar Samkani a lardin Paktia kadai.

  3. 'Iran da Amurka sun amince su rage tashin hankali da ci gaba da tattaunawa'

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani jami’in gwamnatin Amurka ya bayyana cewa Iran da Amurka sun amince su dakatar da kai wa juna hare-hare tare da ci gaba da tattaunawa kan yarjejeniyar zaman lafiya.

    A cewarsa, za a ci gaba da tattaunawa kan dukkan fannoni na yarjejeniyar, yayin da ɓangarorin biyu za su ƙaurace wa ƙara tsananta rikici a halin yanzu, tare da bai wa jiragen ruwa damar zirga-zirga cikin ‘yanci.

    Duk da wannan bayani, har yanzu Iran ba ta tabbatar da rahoton ba.

    A ‘yan kwanakin nan dai, rikici ya ƙara tsananta sakamakon taƙaddama kan tafiyar da mashigar Hormuz, tare da kai wa juna hare-hare tsakanin Iran da Amurka, lamarin da ya ƙara yawan fargabar rushewar tsagaita wutar da ake ƙoƙarin cimmawa.

    Jami’in na Amurka, wanda ya nemi a sakaya sunansa, bai bayyana lokacin da kuma wurin da za a ci gaba da tattaunawar ba, sai dai wasu majiyoyi sun ce ana sa ran ɓangarorin biyu za su sake haɗuwa a Doha, babban birnin Qatar, domin ci gaba da tattaunawa, yayin da kowanne ɓangare ke zargin ɗayan da karya yarjejeniyar da aka cimma a baya-bayan nan.

  4. Za mu ɗauki tsauraran matakai kan duk wanda ya karya yarjejeniya - Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, ya yi gargaɗin cewa ƙasarsa za ta ɗauki tsauraran matakai kan duk wani ɓangare da ya karya yarjejeniyar da aka ƙulla, yana mai cewa irin wannan mataki na iya kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron yankin.

    Araqchi, wanda ya kai ziyara ƙasar Iraki, ya bayyana hakan ne a yayin ganawarsa da Shugaban ƙasar, Nizar Amidi, inda ya ce karya wasu sashe-sashe na yarjejeniyar da Amurka da kuma Isra’ila suka yi musamman sashe na farko ya zama babban tarnaki ga ƙoƙarin dawo da kwanciyar hankali a yankin.

    Ya ƙara da cewa Iran na ƙoƙarin aiwatar da yarjejeniyar cikin gaskiya tare da bin ƙa’idar kowane ɓangare ya cika nauyin da ya rataya a kansa.

    Sai dai ya jaddada cewa Iran ba za ta lamunci duk wani saba yarjejeniyar ba, yana mai nanata cewa za su ɗauki matakan da suka dace domin kare muradun ƙasarsu da kuma tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin.

    Haka kuma, ya yi kira ga sauran ɓangarorin da ke cikin yarjejeniyar da su mutunta alƙawurran da suka ɗauka, yana mai cewa haɗin gwiwa da gaskiya su ne ginshikin warware rikice-rikice da ke addabar yankin Gabas ta Tsakiya.

  5. Assalamu alaikum

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za kuma ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.