'Iran ta yi harbin gargaɗi kan jiragen Amurka'

Asalin hoton, ISNA
Iran ta ce ta harba makamai masu linzami domin yin gargaɗi ga jiragen yaƙin ruwa na Amurka a gaɓar ruwan Oman, inda ta ce jiragen na Amurka na hantarar tankokin mai da ke ratsawa da kuma jiragen ƴan kasuwa.
Sai dai Amurka ta musanta hakan, wadda tun farko ta ce ta tare wani jirgin ruwa da aka ƙaƙaba wa takunkumi, da kuma wani jirgin wanda bai ɗauke da tutar kowace ƙasa a tekun Indiya.
Wani saƙo da aka wallafa ya ce Amurka za ta ci gaba da tare duk wani jirgin ruwa da ke taimaka wa Iran.
A ranar Alhamis, masu lura da sufurin jiragen ruwa sun ce sun lura da cewa jiragen ruwa mallakin Iran da dama sun ratsa ta Mashigar Hormuz dun da iƙirarin toshe tashoshin ruwan Iran da Amurka ta ce tana yi.















