Cutar Ebola ta ɓulla a Faransa

Asalin hoton, Getty Images
Faransa ta sanar cewa ta tabbatar da ɓullar cutar Ebola a ƙasar, bayan wani likita da ya dawo daga aikin jin ƙai a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo (DRC) ya kamu da cutar.
Ma’aikatar lafiyar ƙasar ta ce an garzaya da shi asibiti na musamman cikin gaggawa, kuma yana cikin yanayi mai kyau.
Wannan shi ne karo na farko da aka tabbatar da cutar Ebola a Turai.
Duk da haka, wani likitan Amurka da ya kamu da cutar a DRC ya taba samun magani a Jamus.
Haka kuma, Uganda ta tabbatar da ɓullar cutar, inda aka samu mutane 20 da suka kamu, ciki har da mutum biyu da suka mutu.
An kuma ce cutar ta sake ɓulla a DR Congo a watan da ya gabata, sai dai masana sun yi hasashen cewa ta fara yaɗuwa tun kafin a sanar da ɓarkewar.
Sama da mutane 260 ne suka mutu sakamakon cutar a DR Congo yayin da fiye da 1,000 suka kamu da da ita a ƙasar.
Hukumomin Faransa sun jaddada cewa babu wani haɗarin yaduwar cutar sosai ga jama’a.
Sun kuma ce suna ci gaba da bin diddigin duk wanda ya yi hulɗa da likitan domin hana yaɗuwar cutar, wadda ke yaɗuwa ta hanyar gumi musamman tsakanin ma’aikatan lafiya.



















