Ƙananan yara da mata sun mutu a harin Isra'ila kan Gaza
Kungiyar agaji ta Palestine Red Crescent da kuma wasu majiyoyi daga wani asibiti sun ce wani hari da Isra'ila ta kai kan wani gida da ke Gaza ya yi sanadin rasa rayukan mutum bakwai ciki har da ƙananan yara mata biyu tare da jikkata wasu 15.
Rahotannisun ce wani jirgin yaƙin Isra'ila ne ya harba makamai masu linzami a kan gidan da ke tsakiyar birnin.
Rundunar sojin Isra'ila dai ta ce ta kai wa wasu manya biyu a ƙungiyar Hamas hari a arewacin Gaza, to amma bata bayyana sunayensu ba.
A jiya Laraba Isra'ilan ta hallaka sabon kwamandan Hamas a Gaza wato Mohammed Odeh.
Wannna rikicin dai na zuwa ne duk da yarjejeniya tsagaita wuta da aka amince da ita a watan Oktoban da ya gabata.