PDP tana zaɓen fidda gwani na majalisar dokokin jihohi
Nan gaba a ranar Juma'ar nan ne babbar jam’iyyar adawa ta Najeriya, PDP za ta gudanar da aikin tantance ƴan takarar kujerun majalisun jihohi a faɗin ƙasar.
A baya-bayan nan ne jam’iyyar ta tantance waɗanda za su yi mata takarar kujerun majalisar wakilai da na majalisar dattawa a babban zaɓen 2027.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin cikin gida ke ci gaba da ƙamari, inda tsagin ministan Abuja, Nyesom Wike, shi ma ke gudanar da nasa aikin tantance ƴan takarar.
A yanzu dai jam'iyyar ta PDP ta dare gida biyu tsakanin ɓangaren Tanimu Turaki da kuma ɓangaren da Nyesom Wike ko goya wa baya.