Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da kawo muku muhimman bayanan dangane da wainar da ake toyawa a Najeriya da sassan duniya na 22/05/2026

Rahoto kai-tsaye

Usman MINJIBIR da Nabeela Mukhtar Uba

  1. PDP tana zaɓen fidda gwani na majalisar dokokin jihohi

    Nan gaba a ranar Juma'ar nan ne babbar jam’iyyar adawa ta Najeriya, PDP za ta gudanar da aikin tantance ƴan takarar kujerun majalisun jihohi a faɗin ƙasar.

    A baya-bayan nan ne jam’iyyar ta tantance waɗanda za su yi mata takarar kujerun majalisar wakilai da na majalisar dattawa a babban zaɓen 2027.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin cikin gida ke ci gaba da ƙamari, inda tsagin ministan Abuja, Nyesom Wike, shi ma ke gudanar da nasa aikin tantance ƴan takarar.

    A yanzu dai jam'iyyar ta PDP ta dare gida biyu tsakanin ɓangaren Tanimu Turaki da kuma ɓangaren da Nyesom Wike ko goya wa baya.

  2. Al-Nassr ta lashe Saudi Pro League

    Kungiyar kwallon kafa ta Al-Nassr ta lashe babban gasar kwallon kafa ta Saudiyya (Saudi Pro League) ta farko tun shekarar dubu biyu da sha tara, inda fitaccen dan wasanta Cristiano Ronaldo ya zura kwallaye biyu don taimaka mata wajen lashe wasan karshe na kakar wasan bana.

    Sadio Mane da Kingsley Coman suma sun zura kwallaye daya-daya a cikin hudun da Al-Nassr ta jefa a ragar Damac.

    Nasarar ta sa kungiyar ta kammala gasar bana da maki biyu tsakaninta da Al Hilal a saman teburi.

    Wannan dai shi ne babban kofi na farko da Ronaldo ya lashe tun bayan da ya koma Al-Nassr a shekarar dubu biyu da ashirin da biyu.

  3. Wasu fusatattu mutane sun ƙona asibitin Ebola a DR Congo

    Wasu fusatattun mutane sun kona wani bangare na wani asibiti a gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango bayan mutuwar wani mara lafiya da ake zargin yana dauke da cutar Ebola.

    A Lardin Ituri wani matashi ya mutu bayan ya kamu da Ebola sai yan uwansa suka nemi a basu gawar amma ma'aikatan asibiti suka hana su, sakamakon haka suka tayar da tarzoma.

    Ma’aikatan lafiya a asibitin Rwampara na karkashin kariyar sojoji yayin da ƴan sanda ke kokarin dawo da zaman lafiya.

    Jami’ai sun ce cutar ta kashe mutane sama da dari da hamsin (150), inda ake zargin sama da wasu mutum dari shida (600) sun kamu da cutar.

  4. Ministocin ƙungiyar tsaro ta NATO na taro kan yaƙin Iran

    A ranar Juma'ar nan ne ministocin harkokin wajen ƙungiyar tsaro ta NATO ke taro a ƙasar Sweden a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar takun saƙa a cikin ƙawancen sakamakon da yaƙin Amurka da Iran da kuma tasirinsa a duniya.

    Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, ya shaida wa BBC cewa za a tattauna batun rage yawan sojojin Amurka a Turai.

    Ya ƙara da cewa shugaba Trump ya ji taƙaicin ƙasashen NATO saboda rashin goyon bayansu.

    Tun da farko, Mista Trump ya sanar da cewa zai tura dakaru dubu biyar zuwa Poland, makonni kadan bayan da Washington ta ce ta janye dubban sojoji daga Jamus.

    Ana kuma sa ran ministocin za su tattauna kan ci gaba da goyon bayan Ukraine a yakin da take yi da Rasha

  5. Ɗan majalisar jihar Kano mai wakiltar gwamna ya koma wurin Kwankwaso

    Ɗan majalisar dokokin jihar Kano da ke wakiltar ƙaramar hukumar Gwale, wadda ita ce ƙaramar hukumar gwamnan Kano, Abdulmajid Isa Umar Mai Rigar Fata ya fice daga jam'iyyar APC zuwa ta NDC.

    A ranar Alhamis ne dai tsohon gwamnan jihar Kano, Rabi'u Musa Kwankwaso wanda shi ne jagoran jam'iyyar NDC ya karɓi ɗan majalisar.

    Mai Riga ya sanar da sauya sheƙara tasa ne bayan gaza samun takarar yin tazarce a kujerar tasa a lokacin zaɓen fidda gwani da jam'iyyar APC ta gudanar, bisa zargin "rashin gaskiya da adalci".

    Ana dai ganin nan ba da jimawa ba za a yi ta samun masu sauya sheƙa sakamakon abubuwan da suka faru a jam'iyyu na zaɓen cikin gida.

    Da ma dai wata kotu a Abuja ta dakatar da wa'adin da hukumar zaɓe ta saka wa jam'iyyu dangane da ranakun rufe rijistar ƴaƴan jam'iyyu, wanda ake yi wa kallon shi ma zai ƙara bai wa ƴan siyasa damar ci gaba da sauya sheƙa.

  6. Da gaske Tinubu ya ce zai dakatar da shari'ar Musulunci a Najeriya?

    Fadar shugaban Nijeriya ta musanta wani labari da ta ce na jabu ne, da ya yi zargin cewa Shugaba Bola Tinubu na yunƙurin yi wa tsarin mulkin Nijeriya gyaran fuska domin sauya sunan ƙasar da kuma rusa dokar shari'ar Musulunci.

    Ta ce labarin wanda aka wallafa ba tare da ambatar majiyarsa ba, wani ɓangare ne na "maƙarƙashiyar wasu ƴan siyasa da idonsu ya rufe a ƙoƙarinsu na haddasa ƙiyayya da janyo rikicin siyasa da tunzuri" gabanin babban zaɓen 2027.

    Labarin dai ya bayyana ne a shafukan sada zumunta a makonnin da suka gabata kuma ya sake bayyana a baya-baya nan.

  7. Cuba barazana ce ga tsaron Amurka - Marco Rubio

    Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, ya bayyana cewa, Cuba barazana ce ga tsaron ƙasar Amurka, kuma ya yi gargaɗin cewa abu ne mai wuya a iya warware rikicin da ke tsakanin ƙasasehn biyu cikin lumana.

    Jami'an Cuba dai sun sha zargin Washington da ƙoƙarin nemo hujjar ɗaukar matakin soji a kan tsibirin.

    A ranar Laraba, Washington ta tuhumi tsohon shugaban Cuba Raul Castro da kisan kai sakamakon wani hari da aka kai shekara talatin da suka wuce.

    Amurka ta girke jiragen ruwan yaki a yankin Caribbean, kuma ta kwashe watanni da dama ta na killace tsibirin.

  8. Buɗewa

    Masu bibiyar mu barka da safiyar ranar Juma'a da fatan kun wayi gari lafiya. Kamar kowace rana mun dawo domin ci gaba a inda muka tsaya a shafinmu na kai tsaye da ke kawo muku wainar da ake toyawa dangane da yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da ƙasar Iran.

    Har wayau, shafin yana kuma kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da ma sauran sassan duniya.