Shugaban majalisar dokokin Senegal El Malick ya yi murabus
Shugaban Majalisar Dokokin ƙasar Senegal, El Malick Ndiaye ya yi murabus daga muƙaminsa kwana biyu bayan korar firaminista Ousmane Sonko, lamarin da ya tayar da zargin cewa ana shirin ba Sonko damar komawa cikin majalisa da kuma neman sabon muƙami.
A cikin sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi, Ndiaye ya ce matakin nasa ya samo asali ne daga “zurfin tunani” da kuma “la’akarin kishin ƙasa,” yana mai cewa akwai lokuta da muradin ƙasa ke bukatar fifikon gaskiya kan komai.
Bayan murabus ɗinsa, an kira zaman majalisar dokoki da za a yi a ranar Talata domin shirya mayar da Sonko kujerarsa ta majalisa tare da zaɓen sabon Shugaban Majalisar.
Sonko, wanda shi ne shugaban jam’iyyar PASTEF, ya riga ya lashe kujera a zaɓen 2024 amma ya ajiye ta lokacin da ya zama Firaminista.
Ƙasar Senegal na fuskantar sabon yanayin siyasa, inda ake ganin dangantaka tsakanin Shugaba Bassirou Diomaye Faye da Sonko na iya kawo canji ga ikon gwamnati, musamman ganin jam’iyyar PASTEF na da rinjaye a majalisa, abin da ke ƙara haifar da rashin tabbas kan yadda sabuwar gwamnati za ta gudanar da mulki.