Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya buƙaci ƙasashen Afirka su ɗauki wasu matakai domin inganta haɗin kai da tsaron nahiyar.
Shugaba Tinubu, wanda mataimakinsa Kashim Shettima ya wakilta a taron AU a aka gudanara a Luada, ya bayyana wasu shawarwari da ya ce idan nahiyar ta ɗauka za u taimaka mata.
- Kawo ƙarshen rikice-rikice
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa ya kamata Afirka ta ɗauki mataki na ƙashin kanta wajen kawo ƙarshen rikice-rikicen da ake a wasu ƙasashen Afirka ciki har da Najeriya, kamar yadda ɗaya daga cikin masu magana da yawun shugaba Tinubun Abdulaziz Abdulaziz ya shaida wa BBC.
Haka kuma ya nemi haɗin kan kasashen Afirka wajen magance matsalolin tsaro da ke damun wasu ƙasashen Afrika .
Bola Ahmed Tinubu, ya ce Najeriya ta goyi bayan amincewa da shirin aiki na Luanda, inda ya bayyana shi a matsayin wata hanya mai amfani ta ƙarfafa matakan hana barkewar rikice-rikice.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce hana rikice-rikice tun kafin su auku ya fi sauki kuma ya fi ɗorewa fiye da ƙoƙarin magance su bayan sun ɓarke.
- Rage dogaro kan wasu ƙasashe
Abdulaziz Abdulaziz, ya ce shugaban na Najeriya ya buƙaci a rage yawan dogaron da ake yi kan wasu ƙasashe domin kawo wa Afirka ɗauki.
''Ya ce yawan dogaron da ake musammam a ɓangaren tsaro, na iya raunana hanyoyin ƙungiyar AU wajen hana rikice-rikice da kuma manufar cewa 'yan Afirka ne ya kamata su jagoranci warware matsalolinsu."
Tinubu ya kuma yi kira ga ƙasashen da ke ƙera da fitar da makamai su ƙara haɗa kai da sauran ‚ƴan'uwansu na Afirka wajen samar ko kuma ƙera makamai domin amfanin kasashensu.
Shugaba Tinubu ya buƙaci shugabannin Afirka su sake jajircewa wajen samar da mafita ta cikin gida, da ƙarfafa haɗin gwiwa, da kuma raba alhakin tunkarar ƙalubalen tsaron da ke addabar nahiyar.