Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 9/08/2026

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Lahadi 9 ga watan Agustan 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. An ayyana dokar ta-ɓaci kan gobarar daji a yammacin Canada

    An ayyana dokar ta-baci a lardin British Columbia da ke yammacin Kanada, bayan gobarar daji da ta gagara kashewa ta tilasta wa dubban mutane tserewa daga gidajensu.

    Shugaban gwamnatin lardin, David Eby, ya bukaci duk mutumin da aka umarta na yatashi , da ya gaggauta tashi nan take, yana mai gargaɗin cewa gobarar na ci gaba da bazuwa cikin sauri sosai.

    Ya ce gobarar ta lalata wasu gidaje da kadarori, yayin da aka ceto wasu mazauna da suka makale sakamakon yadda wutar ta kewaye su.

    Garin Summerland da ke kudancin lardin na daga cikin yankunan da abin ya fi shafa, inda wutar ke ta ci ganga-ganga ba kakkautawa tun ran Juma.a Jami'ai sun ce gobarar, yanzu ta mamaye fiye da fili mai fadin murabba'in kilomita 100.

  2. FIFA ta yi zargin akwai wasu shirya muzanta shugabanta Infantino

    Hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya, FIFA, ta yi tsayin daka wajen kare shugabanta Gianni Infantino, tana mai cewa akwai wani “tsari da aka shirya kuma ake ci gaba da aiwatarwa daga wasu ɓangarori” domin muzanta shi.

    Wakilin BBC ya ce Gianni Infantino ya sha bincike da dama a lokacin shugabancinsa na shekara goma.

    Shugaban na fuskantar suka a cikin makon nan bayan ya yi watsi da shirinsa na sayar da hannun jari a bangaren wasan cin kofin duniya, ga masu zuba jari.

    Tun da farko, FIFA ta ce Mista Infantino ya yi fatali da zarge-zargen da ke cewa hukumar kwallon kafa ta Turai, UEFA ta biya wata mata da ake bayyana a matsayin wadda ake zargin tana da alaƙa ta soyayya da shi, a lokacin da yake jagorantar hukumar ƙwallon ta Turai.

    UEFA ta ce kuɗin da aka biya matar ya yi daidai da ƙa’idojin da ke aiki a lokacin. Sai dai hukumar ta ƙara da cewa an ƙara tsaurara waɗannan ƙa’idoji tun daga lokacin.

  3. An yi jana’izar mutum 16 da aka kashe a wani hari a Benue

    An gudanar da jana’izar jama’a a ranar 8 ga watan Agusta a ƙauyen Efeyi da ke jihar Benue, arewa ta tsakiyar Najeriya, inda aka yi wa mutum 16 da ake zargin wasu ƴanbindiga suka kashe jana’iza, kamar yadda jaridar Vanguard mai zaman kanta ta ruwaito.

    Rahotanni sun ce an kashe mutanen ne lokacin da aka kai hari a ƙauyen a ranar 28 ga watan Yuli, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin firgici tare da tilasta wa da dama daga cikinsu tserewa domin tsira da rayukansu.

    Mazauna kauyen sun bayyana harin a matsayin mummunan hari da aka kai ba tare da wani dalili ba.

    Harin ya faru ne watanni bayan da wasu ‘yan bindiga suka kashe mutane da dama a wasu kauyuka da ke cikin gundumar Ugboju, a ƙaramar hukumar Otukpo.

    A wajen jana’izar, ’yan uwa, shugabannin al’umma, sarakunan gargajiya, shugabannin siyasa da malaman addini sun hallara domin yin bankwana da wadanda aka kashe.

    Wani limamin Cocin Katolika ne ya jagoranci addu’o’in jana’izar, kafin a sauke akwatunan gawarwakin wadanda aka kashe cikin kaburburansu, yayin da ’yan uwa da makusanta ke kuka da alhini.

    Jihar Benue, wadda ke yankin Middle Belt na Najeriya, na fama da rikice-rikice da suka samo asali musamman daga hare-haren ramuwar gayya da satar shanu tsakanin makiyaya, wadanda galibinsu Musulmi ne, da manoma, wadanda galibinsu Kiristoci ne.

  4. An jefa bama-bamai a Colombia ranar da sabon shugaban ƙasa ya kama aiki

    An kai hare-haren bama-bamai biyu a Colombia a ranar farko da sabon shugaban ƙasar mai ra'ayin mazan jiya, Abelardo de la Espriella, ya kama aiki.

    Rundunar sojin kasar ta dora alhakin ɗaya daga cikin hare-haren kan wasu mayaƙan ƙungiyar FARC da suka balle daga yarjejeniyar sulhu.

    Daya daga cikin fashewar ta lalata wurin karɓar kuɗin hanya a kusa da birnin Cali, inda aka gudanar da bikin rantsar da shugaban ƙasar a shekaran jiya Juma’a.

    Jami’an tsaro biyu sun jikkata sakamakon harin. A wani hari na biyu da aka kai kan wani caji ofis da jirgin sama maras matuki a gundumar Cesar da ke arewacin ƙasar, an kashe wani ɗan sanda.

    Shugaba Abelardo de la Espriella, wanda ya sha alwashin ɗaukar tsauraran matakai kan abin da ya kira “ta’addancin masu safarar miyagun ƙwayoyi”, ya ce waɗanda suka kai hare-haren ba za su samu mafaka a ko’ina ba.

  5. Mayaƙan Houthi sun kai hari kan matatar man fetur ta Saudiyya

    Mayaƙan Houthi na Yemen sun ce sun kai harin jirgin sama mara matuƙi kan wata matatar man fetur ta Saudiyya da ke gaɓar Bahar Maliya.

    Kakakin rundunar sojin ƙungiyar, Yahya Saree, ya ce harin da aka kai kan matatar man fetur ta Aramco da ke Jazan, martani ne kan kutsen da Saudiyya ke yi a arewa maso yammacin Yemen.

    Ma'aikatar makamashi ta Saudiyya ta ce jami'an kashe gobara sun yi nasarar kashe gobarar da ta tashi a wurin.

    Mayaƙan Houthi sun sanar da kafa katanga ta ruwa kan Saudiyya a watan da ya gabata, lamarin da ya sake rura wutar rikicin tare da ƙara matsin lamba kan samar da makamashi a duniya, wanda yaƙin Iran ya haifar.

    A gefe guda kuma, babbar hukumar tsaron Iran ta yi gargadin cewa ba za a bude mashigar ruwan Hormuz ba har sai Amurka ta amince da wasu bukatu guda shida, ciki har da sassauta takunkuman da aka ƙaƙaɓawa Iran, biyan diyya kan barnar yakin, da kuma kawo karshen katangar da aka sanya wa tashoshin jiragen ruwa na Iran.

  6. Mutum 22 sun rasu a haɗarin mota a Nijar

    Mahukunta a Nijar sun ce aƙalla mutum 22 ne suka rasu, wasu kusan 40 kuma suka ji rauni bayan wasu motocin bas biyu sun yi taho-mu-gama a kusa da garin Madawa da ke kudancin ƙasar.

    Ma’aikatar Sufuri ta Nijar ta ce aƙalla mutum 17 daga cikin waɗanda suka mutu sojoji ne da ke tafiya a ɗaya daga cikin motocin.

    Har yanzu ba a san musabbabin haɗarin ba, amma jami’ai sun ce ana ci gaba da bincike domin gano abin da ya haddasa afkuwar lamarin.

    Hatsarin ya faru ne a daidai lokacin da hukumomin Nijar ke gudanar da shiri na wayar da kan jama’a kan bin dokokin kiyaye haɗurran hanya.

    Haɗurran hanya na yawan afkuwa a kan titunan ƙasar ta Nijar, wadda ke yankin Sahel mai faɗin gaske, inda sama da mutum 1,200 suka mutu sakamakon irin waɗannan haɗurra a shekarar da ta gabata - 2025

  7. Farawa

    Jama'a masu bibiyar wannan shafi na kai-tsaye daga BBC Hausa.

    A wannan shafi za mu ci gaba da kawo muku labaran abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na Facebook da X da kuma Whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.