KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 9/08/2026

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Lahadi 9 ga watan Agustan 2026.

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. An yi jana’izar mutum 16 da aka kashe a wani hari a Benue

    Ƴanbindiga

    Asalin hoton, Getty Images

    An gudanar da jana’izar jama’a a ranar 8 ga watan Agusta a ƙauyen Efeyi da ke jihar Benue, arewa ta tsakiyar Najeriya, inda aka yi wa mutum 16 da ake zargin wasu ƴanbindiga suka kashe jana’iza, kamar yadda jaridar Vanguard mai zaman kanta ta ruwaito.

    Rahotanni sun ce an kashe mutanen ne lokacin da aka kai hari a ƙauyen a ranar 28 ga watan Yuli, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin firgici tare da tilasta wa da dama daga cikinsu tserewa domin tsira da rayukansu.

    Mazauna kauyen sun bayyana harin a matsayin mummunan hari da aka kai ba tare da wani dalili ba.

    Harin ya faru ne watanni bayan da wasu ‘yan bindiga suka kashe mutane da dama a wasu kauyuka da ke cikin gundumar Ugboju, a ƙaramar hukumar Otukpo.

    A wajen jana’izar, ’yan uwa, shugabannin al’umma, sarakunan gargajiya, shugabannin siyasa da malaman addini sun hallara domin yin bankwana da wadanda aka kashe.

    Wani limamin Cocin Katolika ne ya jagoranci addu’o’in jana’izar, kafin a sauke akwatunan gawarwakin wadanda aka kashe cikin kaburburansu, yayin da ’yan uwa da makusanta ke kuka da alhini.

    Jihar Benue, wadda ke yankin Middle Belt na Najeriya, na fama da rikice-rikice da suka samo asali musamman daga hare-haren ramuwar gayya da satar shanu tsakanin makiyaya, wadanda galibinsu Musulmi ne, da manoma, wadanda galibinsu Kiristoci ne.

  2. An jefa bama-bamai a Colombia ranar da sabon shugaban ƙasa ya kama aiki

    Colombia

    Asalin hoton, Getty Images

    An kai hare-haren bama-bamai biyu a Colombia a ranar farko da sabon shugaban ƙasar mai ra'ayin mazan jiya, Abelardo de la Espriella, ya kama aiki.

    Rundunar sojin kasar ta dora alhakin ɗaya daga cikin hare-haren kan wasu mayaƙan ƙungiyar FARC da suka balle daga yarjejeniyar sulhu.

    Daya daga cikin fashewar ta lalata wurin karɓar kuɗin hanya a kusa da birnin Cali, inda aka gudanar da bikin rantsar da shugaban ƙasar a shekaran jiya Juma’a.

    Jami’an tsaro biyu sun jikkata sakamakon harin. A wani hari na biyu da aka kai kan wani caji ofis da jirgin sama maras matuki a gundumar Cesar da ke arewacin ƙasar, an kashe wani ɗan sanda.

    Shugaba Abelardo de la Espriella, wanda ya sha alwashin ɗaukar tsauraran matakai kan abin da ya kira “ta’addancin masu safarar miyagun ƙwayoyi”, ya ce waɗanda suka kai hare-haren ba za su samu mafaka a ko’ina ba.

  3. Mayaƙan Houthi sun kai hari kan matatar man fetur ta Saudiyya

    Houthi

    Asalin hoton, Getty Images

    Mayaƙan Houthi na Yemen sun ce sun kai harin jirgin sama mara matuƙi kan wata matatar man fetur ta Saudiyya da ke gaɓar Bahar Maliya.

    Kakakin rundunar sojin ƙungiyar, Yahya Saree, ya ce harin da aka kai kan matatar man fetur ta Aramco da ke Jazan, martani ne kan kutsen da Saudiyya ke yi a arewa maso yammacin Yemen.

    Ma'aikatar makamashi ta Saudiyya ta ce jami'an kashe gobara sun yi nasarar kashe gobarar da ta tashi a wurin.

    Mayaƙan Houthi sun sanar da kafa katanga ta ruwa kan Saudiyya a watan da ya gabata, lamarin da ya sake rura wutar rikicin tare da ƙara matsin lamba kan samar da makamashi a duniya, wanda yaƙin Iran ya haifar.

    A gefe guda kuma, babbar hukumar tsaron Iran ta yi gargadin cewa ba za a bude mashigar ruwan Hormuz ba har sai Amurka ta amince da wasu bukatu guda shida, ciki har da sassauta takunkuman da aka ƙaƙaɓawa Iran, biyan diyya kan barnar yakin, da kuma kawo karshen katangar da aka sanya wa tashoshin jiragen ruwa na Iran.

  4. Mutum 22 sun rasu a haɗarin mota a Nijar

    Mahukunta a Nijar sun ce aƙalla mutum 22 ne suka rasu, wasu kusan 40 kuma suka ji rauni bayan wasu motocin bas biyu sun yi taho-mu-gama a kusa da garin Madawa da ke kudancin ƙasar.

    Ma’aikatar Sufuri ta Nijar ta ce aƙalla mutum 17 daga cikin waɗanda suka mutu sojoji ne da ke tafiya a ɗaya daga cikin motocin.

    Har yanzu ba a san musabbabin haɗarin ba, amma jami’ai sun ce ana ci gaba da bincike domin gano abin da ya haddasa afkuwar lamarin.

    Hatsarin ya faru ne a daidai lokacin da hukumomin Nijar ke gudanar da shiri na wayar da kan jama’a kan bin dokokin kiyaye haɗurran hanya.

    Haɗurran hanya na yawan afkuwa a kan titunan ƙasar ta Nijar, wadda ke yankin Sahel mai faɗin gaske, inda sama da mutum 1,200 suka mutu sakamakon irin waɗannan haɗurra a shekarar da ta gabata - 2025

  5. Farawa

    Jama'a masu bibiyar wannan shafi na kai-tsaye daga BBC Hausa.

    A wannan shafi za mu ci gaba da kawo muku labaran abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na Facebook da X da kuma Whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.