Jami'an tsaro sun miƙa Bello Badejo ga hukumar EFCC - Hadiminsa

Asalin hoton, OTHERS
Jami'an tsaron Najeriya da suka kama ɗantakarar Sanatan Taraba ta tsakiya a jam'iyar APC, Bello Bodejo, sun miƙa shi ga hukumar yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasar ta'annuti EFCC.
A kama Badejo, wanda shi ne shugaban ƙungiyar Fulani ta Miyetti Allah Kautal Hore, a daren Alhamis bayan ya sauka a filin jirgin sama na Danbaba Suntai da ke birnin Jalingo a jihar.
Hadimin Badejo, Malam Umar, ya shaida wa Daily Trust cewa magoya bayansa ne suka raka shi zuwa ofishin jami'an tsaron da suka kama shi, amma bai bayyana ko su wane ne ba.
Umar ya ce tuntuni jami'an suka kai Badejo ofishin EFCC da ke Abuja, kuma babu wani ƙarin bayani da aka yi musu game da dalilin kama shi.
Ya yi zargin cewa wasu abokan hamayyarsa ne suka kitsa kama shi saboda farin jinishi a takarar.
"Yanzu haka ana tantance ƴantakarar jam'iyar kuma an kusa kammalawa. Manufarsu ita ce su hana shi shiga tantancewar," in ji Umar.
Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan'adam ta Amnesty International ta yi kira hukumomin Najeriya su saki ɗantakarar Sanatan, kamar yadda ta bayyana a wata sanarwa.
















