KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 01/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku bubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 01 ga watan Yulin 2026

Skip Bidiyo and continue reading
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Kutama
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Najeriya za ta nemi diyya kan kasuwanci da dukiyoyin ‘yan ƙasarta a Afirka ta Kudu

    ...

    Asalin hoton, Bayo Onanuga/X

    Gwamnatin Najeriya ta ce za ta nemi a biya diyya kan dukiyoyi da kasuwancin ‘yan ƙasarta da suka bari a Afirka ta Kudu yayin da ake dawo da su gida sakamakon hare-haren nuna kyamar baƙi.

    Muƙaddashin babban jakadan Najeriya a Afirka ta Kudu, Alexander Ajayi ne ya bayyana haka yayin wata tattaunawa da ya yi da Gidan talabijin na Channels inda ya ce gwamnati ta fara tattara bayanai kan dukiyoyin da ‘yan kasar suka bari, domin tuntubar gwamnatin Afirka ta Kudu kan yadda za a biya diyya.

    Ya ce an buƙaci ‘yan Najeriyan da ke dawowa su rubuta cikakken bayanin kadarorinsu da suka hada da kasuwanci da motoci da sauran dukiyoyi, yana mai cewa shirin ba zai tsaya ga dawo da su gida kawai ba, gwamnati na kuma da ƙudurin kare jarin ‘yan kasarta.

    A gefe guda kuma, wasu karin ‘yan Najeriya 271 sun isa filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Legas, bayan kwaso su daga Afirka ta Kudu, inda suka gargaɗi sauran ‘yan kasa da su guji zuwa can, suna mai cewa yanayin tsaro ya ƙara taɓarɓarewa sakamakon hare-haren nuna kyamar baƙi.

    A jiya ne dai wasu ‘yan Afirka ta Kudu suka gudanar da zanga-zangar kyamar baki bayan cikar wa’adin da aka ba ‘yan kasashen waje da ba su da takaddar zama a ƙasar su fice, lamarin da ya ƙara tayar da hankula a kasar.

  2. Ruwan sama mai ƙarfi ya haddasa ambaliya a sassan jihar Legas

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ruwan sama mai ƙarfi da aka shafe sa’o’i ana yi a ranar Talata ya haddasa ambaliya a sassa daban-daban na birnin Legas, lamarin da ya janyo tsaiko ga zirga-zirgar jama’a tare da jefa mazauna da dama cikin matsala.

    Gwamnatin Jihar ta bukaci mazauna su kwantar da hankulansu, tana mai cewa tana sa ido kan halin da ake ciki da kuma kokarin shawo kan matsalar ambaliyar da ta sake kunno kai a makonnin baya-bayan nan.

    Kwamishinan muhalli da albarkatun ruwa na jihar, Tokunbo Wahab, ya bayyana cewa ruwan saman ya zo da tsananin yawa cikin kankanin lokaci, wanda ya haddasa cunkoso a magudanan ruwa tare da janyo ambaliya a yankuna kamar Victoria Island, Lekki, Ikeja, Gbagada, Mushin da Mafoluku.

    Ya kuma ce ba Legas kadai irin wannan ruwan sama mai ƙarfi ya shafa ba, domin an samu makamancin haka a wasu sassan Afirka da ma Arewacin Amurka.

    Gwamnatin ta kuma gargaɗi jama’a da su guji zubar da shara a magudanan ruwa da kuma gina gine-gine a wuraren da ke hana ruwa gudana domin rage illar ambaliya a gaba.

  3. Za a rufe Tehran ranar Talata saboda jana’izar Ayatollah Khamenei

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Iran ta sanar da cewa za a rufe babban birnin kasar, Tehran, a ranar Talata 6 ga watan Yuli, domin saukaka gudanar da jana’izar Ayatollah Ali Khamenei da kuma bai wa masu makoki damar fita daga birnin cikin sauki bayan halartar bukukuwan.

    Mai magana da yawun gwamnatin, Fatemeh Mohajerani, ta ce an ɗauki wannan mataki ne domin taimakawa wajen sauƙaka zirga-zirgar dubban mutanen da suka halarci jana’izar jagoran addinin ƙasar.

    Ta kuma bayyana cewa an ayyana ranar Alhamis a matsayin ranar zaman makoki a faɗin Iran baki ɗaya.

    Ana sa ran binne Ayatollah Ali Khamenei a birnin Mashhad ranar Alhamis 8 ga watan Yuli.

    An tsara gudanar da jana’iza da binne shi a biranen Tehran, Qom da Mashhad daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Yuli.

    Haka kuma, za a gudanar da wasu bukukuwan tunawa da shi a biranen Bagadaza, Kazmin, Karbala da Najaf a ƙasar Iraq.

    Ayatollah Ali Khamenei ya rasu ne sakamakon hare-haren saman daAmurka da Isra’ila suka kai kan Iran, inda suka kai harin a gidansa sai dai har yanzu ba a binne shi ba.

  4. Assalamu alaikum!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Laraba daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.