KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 23 ga watan Yunin 2026.

Skip Bidiyo and continue reading
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Kutama
  • xxx
  • Sadis Buba

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. NAHCON ta kammala jigilar Alhazan Najeriya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar alhazai ta Najeriya NAHCON ta ce a hukumance ta kammala jigilar alhazan Najeriya sama da 38,000 da suka tafi ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2026.

    Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar NAHCON, Hajiya Fatimah Usara ta fitar ta ce ana sa ran jirgin ƙarshe ɗauke da alhazai daga Jihar Zamfara zai iso Najeriya a ranar Talata.

    Usara ta ce kammala jigilar ya kawo ƙarshen ayyukan Hajjin 2026.

    Sai dai ta ce alhazan Najeriya 12 a halin yanzu suna jinya a asibitoci daban-daban na ƙasar Saudiyya saboda wasu matsalolin lafiya.

    “NAHCON na bin diddigin halin da suke ciki, kuma ta shirya yadda za a dawo da su Najeriya lafiya da zarar an sallame su daga asibitoci.'' in ji ta

    Usara ta ce, an ɗauki darassa masu ma’ana daga wannan aikin Hajjin bana, wanda za a yi amfani da su wajen inganta ayyukan Hajji da za su biyo baya.

    Ta ce a bisa ƙudirin hukumar na ci gaba da inganta ayyukanta da kuma fara shiri tun da wuri, ta fara shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2027 a hukumance.

  2. Trump na sa ran kyakkyawar dangantaka da Colombia a ƙarƙashin sabon shugaba

    ...

    Asalin hoton, Mauricio Dueñas Castañeda, EPA/Shutterstock

    Shugaban Amurka Donald Trump ya yi hasashen samun "dangantaka mai aminci" tsakanin gwamnatinsa da Colombia bayan sakamakon farko na zaɓen da aka gudanar ya nuna cewa ɗan takarar mai ra'ayin mazan jiya Abelardo de la Espriella ne ya lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar ranar Lahadi.

    Ƙidayar kuri’u na farko ya nuna de la Espriella ya doke abokin hamayyarsa, Iván Cepeda, da wani ratan da bai kai kashi ɗaya cikin 100 ba.

    Har yanzu Cepeda bai amince da sakamakon ba, yana mai cewa zai jira a tantance sakamakon tukunna, wanda ya kan ɗauki kwanaki da dama.

    Trump dai ya goyi bayan de la Espriella gabanin zaɓen zagaye na biyu kuma ya bayana Cepeda a matsayin "Mai tsattsaurar ra'ayi".

    Da yake magana da manema labarai a ranar Litinin, Trump ya ce de la Espriella “ya yi nasara cikin sauki”, duk da cewa nasarar da ya samu na kashi 0.96 cikin 100 a ƙidayar farko ita ce mafi ƙanƙanta a tarihin Colombia.

  3. Gwamnati za ta ci gaba da gudana yayin da Starmer ya ke Firaminista - Downing Street

    ...

    Asalin hoton, EPA/Shutterstock

    Gwamnatin Birtaniya ta sanar da cewa ba za a ɓullo da wasu sabbin "manyan manufofi" ko yanke shawarar kashe kuɗi ba yayin da ake shirin mika mulki ga sabon Firaminista.

    Keir Starmer ya faɗawa taron majalisar ministoci da safiyar yau cewa yana son miƙa mulki cikin tsari kuma zai ba da cikakken goyon bayansa ga magajinsa.

    Shugaban ma’aikata na ƙasar ya rubutawa shugabannin ma’aikatun gwamnati cewa su bi tsarin da aka kafa na sauya firaminista.

    "Firaministan ya amince da cewa ba za a ɓullo da wata sabuwar manufa ko shirin kashe kudi da za a fara a wannan lokacin ba," in ji mai magana da yawunsa.

    Amma - mafi mahimmanci - wannan bai nuna ya haɗa da shirin zuba jari na tsaro da aka jinkirta ba, wanda ministocin suka nace cewa za a wallafa shi kafin taron Nato a ranar 7 ga Yuli.

    Da aka tambaye shi ko haramcin sabbin sanarwar manufofin yana nufin gwamnati ta fuskanci dakatarwa, kakakin ya ce ministocin suna nan a kan kujerunsu kuma "ayyukan gwamnati na ci gaba da gudana".

  4. Dole ne Iran ta kashe kuɗin da za mu sakar mata a cikin Amurka - Trump

    xxx

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya sake nanata cewa duk wani kuɗin Iran da aka riƙe, wanda za a saki sanadiyyar ɗage takunkumai da gwamnatin Amurka ta yi, za a tura kuɗin ne zuwa cikin wani asusu na musamman wanda ke ƙarƙashin kulawar Amurkar.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafin sada zumunta, Mista Trump ya ce daga cikin asusun ne Iran za ta iya amfani da kuɗin wajen sayen abinci da magunguna, kuma daga Amurka kawai za ta saya.

    A baya Iran ta yi watsi da sharuɗɗa makamantan haka daga mataimakin shugaban Amurka J.D Vance wanda ya jagoranci tattaunawar sasanci da Iran a ƙasar Switzerland.

    Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya a birnin Geneva ya ce Iran ce kadai take da ƴancin tantance yadda za ta yi, da kuma abin da za ta yi da kadarorinta da za a saki.

  5. Tallafin cutar HIV da Amurka ta cire a Afirka ta Kudu na iya janyo asarar rayuka - MDD

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban hukumar kula da cutar HIV ta Majalisar Ɗinkin Duniya ya yi gargaɗin cewa matakin da Amurka ta ɗauka na janye ɗaukacin tallafin da take bayarwa kan cutar HIV a Afirka ta Kudu na iya haifar da asarar rayuka.

    Shugabar UNAids Winnie Byanyima ta shaida wa manema labarai gabanin taron Majalisar Dinkin Duniya kan cutar, cewa matakin na Amurka na iya jefa waɗanda ke ɗuek da cutar cikin mawuyacin hali.

    Afirka ta Kudu ba ta dogara kan tallafin da Amurka ke ba wa ta fannin magungunan cutar ba, amma Amurka ta ba da gudummawa sosai ga shirye-shiryen ƙasar na hana yaɗuwarta.

    Jami'an Amurka sun shaida wa BBC cewa rage tallafin wani ɓangare ne martanin Amurka kan rashin kare rayukan al'ummar farar fata da ake zargin gwamnatin Afirka ta Kudu ta gaza.

    Zargi da Pretoria ta musanta.

    Ma'aikatar lafiya ta Afirka ta Kudu ta mayar da martani da cewa duk da cewa ba a sanar da ita wannan matakin a hukumance ba, amma ta daɗe tana aiki kan shirin dogaro da kai.

  6. Shugaban Iran Masoud Pezhkian ya isa Pakistan domin ziyarar diflomasiyya

    ....

    Asalin hoton, IRNA

    Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezhkian, ya isa Pakistan domin wata ziyarar kwana ɗaya, inda zai gana da manyan shugabannin ƙasar.

    Bayan isarsa, ya gana da firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif, a cikin ci gaba da tattaunawar diflomasiyya tsakanin ƙasashen biyu.

    Haka kuma, Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ya isa Pakistan domin haɗuwa da shugaban ƙasar a wannan ziyara, bayan ya fito daga Oman inda ya je tattaunawa kan yadda za a tafiyar da mashigar Hormuz.

    Araqchi ya je Oman ne daga Switzerland, inda ya halarci tattaunawar sulhu da aka yi tsakanin Iran da Amurka, tare da wata tawagar Iran da ta haɗa da kakakin majalisar dokoki Mohammad Baqer Qalibaf.

    Kafin isowar shugaban ƙasar Iran, Araqchi ya gana da Shugaban Pakistan da firaminista a Islamabad a wani ɓangare na shirye-shiryen ziyarar.

  7. Ba ma da shirin bai wa IAEA damar binciken tashoshinmu na nukiliya – Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran ta ce ba ta da wani shiri a halin yanzu na bai wa Hukumar Kula da Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) damar binciken cibiyoyinta na nukiliya da suka lalace sakamakon yaƙi.

    Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai, inda ya ce babu wata yarjejeniya da ta tanadi irin wannan batu.

    Ya ce Iran za ta ci gaba da bin tsarin da take amfani da shi a yanzu a karkashin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT) da kuma dokokin kulawa da makaman nukiliya.

    “Gaba ɗaya babu wata doka ko tsari a kan wannan batun. A matsayinmu na mamba a yarjejeniyar NPT, za mu ci gaba da bin hanyoyin da muke kai yanzu, kuma tsarin a bayyane yake,” in ji Baghaei.

    Hakazalika, ya ce babu wata ganawa da aka shirya tsakaninsa da babban daraktan IAEA, Rafael Grossi, a Switzerland.

    Wannan bayani na Iran ya zo ne bayan kalaman Mataimakin Shugaban Amurka, JD Vance, wanda ya bayyana cewa Iran ta amince a ba masu binciken damar bincikar cibiyoyin nukiliyarta.

    Sai dai gwamnatin Iran ta musanta wannan ikirari, tana mai cewa ba ta ɗauki wani sabon alƙawari dangane da batun binciken nukiliya ba, kuma hulɗarta da IAEA za ta ci gaba ne a ƙarƙashin dokokin da ake da su.

  8. Wani abun fashewa ya tashi a wata kasuwa dake Lagos

    ....

    Asalin hoton, Screengrab/Lagos Police Command

    Wani abun fashewa ya tashi a wani sashe na kasuwar Mushin da ke Lagos a ranar Litinin, inda mutum guda ya jikkata bayan wata mota ta tarwatse sakamakon fashewar.

    Lamarin ya faru ne da tsakar dare a wani wuri da ke 22, Oke Mushin, inda aka ajiye motar a cikin kasuwar kayan takalma.

    Mazauna yankin sun bayyana cewa ana zargin wani ne ya dasa abun fashewa (IED) a ƙarƙashin motar da ta tarwatse, amma har yanzu ba a gano mamallakin motar ba.

    Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Fatai Tijani, ya ce sun samu rahoton fashewar, kuma nan take suka tura ƙwararrun jami’an kwance abubuwan fashewa (EOD) zuwa wurin.

    Ya ƙara da cewa binciken farko ya nuna cewa an sanya IED ɗin ne a ƙarƙashin motar a ɓangaren fasinja, kuma ya fashe ne a lokacin da aka kunna injin motar.

  9. Qalibaf da Araqchi sun tafi Oman kan batun Mashigar Hormuz

    Shugaban majalisar dokokin Iran, Mohammad Baqer Qalibaf, tare da babban mai shiga tsakani Abbas Araqchi, sun tafi ƙasar Oman domin tattaunawa kan yadda za a tafiyar da Mashigar Hormuz.

    Rahotanni sun ce Qalibaf ya bar Tehran zuwa Muscat jim kadan bayan dawowarsa daga tattaunawar Iran da Amurka da aka yi a Switzerland, inda batun sarrafa mashigar ya zama muhimmin abu.

    Ana sa ran tawagar Iran za ta gana da Sarkin Oman, Haitham bin Tariq, domin tattauna shirye-shiryen Iran kan kula da mashigar da kuma karfafa hadin gwiwar ƙasashen biyu.

    Wannan na zuwa ne bayan kammala zagayen farko na tattaunawar Iran da Amurka, wanda ya sa tawagar Iran komawa gida kafin sake wasu muhimman ganawa.

    A wani ɓangare kuma, fadar shugaban Iran Masoud Pezeshkian ta sanar da cewa zai kai ziyara Pakistan na kwana guda, domin gode wa kokarin sasanci da kasar ta yi tsakanin Iran da Amurka tare da bunƙasa hulɗar tattalin arziki.

  10. Sojojin Najeriya sun ce sun kuɓutar da mutane 47 daga hannun ISWAP a Borno

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation Hadin Kai a yankin Arewa maso Gabas ta ceto mutum 47, yawancinsu mata da ƙananan yara, da mayaƙan ISWAP suka tsare a yankin Kangarwa da ke ƙaramar hukumar Kukawa a jihar Borno.

    A cikin sanarwar da rundunar ta fitar, ta bayyana cewa an samu nasarar ceto mutanen ne a ranar 20 ga watan Yuni 2026, bayan wani gagarumin samame da sojojinta suka kai wanda ya tilasta ‘yan ta’addar tserewa suka bar waɗanda suka sace.

    Ya ce hare-haren kasa da na sama da dakarun suka kai wa sansanonin ISWAP a yankin Tafkin Chadi ne ya sa ‘yan ta’addar suka rikice suka bar wuraren da suke, lamarin da ya bai wa wadanda aka tsare damar tsira bayan dogon lokaci a hannunsu.

    A yanzu haka, an kai waɗanda aka ceto wuraren tsaro inda ake basu kulawar lafiya da taimakon jin kai, yayin da rundunar ta sake jaddada ƙudurinta na ci gaba da kawo ƙarshen ayyukan ta’addanci da dawo da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.

  11. Iran ta nace kan ci gaba da iko da Mashigar Hormuz

    ....

    Asalin hoton, Tasnim news agency

    Iran ta sake jaddada ƙudurinta na ci gaba da iko da Mashigar Hormuz bayan kammala zagayen farko na tattaunawa da Amurka a ƙasar Switzerland.

    Da yake magana da talabijin din gwamnatin Iran yayin dawowarsa daga tattaunawar, babban mai shiga tsakani na ƙasar ya bayyana cewa tafiyar da mashigar ba za ta koma yadda take kafin yaƙin ba.

    Ya ce Iran za ta ci gaba da taka rawa wajen sarrafa zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin, tare da tabbatar da cewa an kiyaye buƙatun ƙasar.

    Haka kuma, ya bayyana cewa Iran da Amurka sun amince da kafa wasu hanyoyin haɗin gwiwa na wucin gadi na kwana talatin, ciki har da layin waya kai tsaye da cibiyar sadarwa, domin sauƙaka zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar.

    A nasa ɓangaren, sakataren kudi na Amurka Scott Bessent ya ce Washington za ta dakatar da takunkumin da ta kakabawa man Iran na tsawon kwanaki sittin, domin bai wa tattaunawar damar ci gaba.

  12. Za a samu mummunan yanayin zafi a Turai yau

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ana sa ran mummunan yanayin zafi zai addabi sassan Yammacin Turai a yau Talata, inda zafin zai kai matakin da aka daɗe ba a gani ba a tarihi.

    Masana hasashen yanayi sun ce zafin zai ƙara tsanani a wannan makon lamarin da ke haddasa fargaba a ƙasashe da dama.

    A Faransa, an gargaɗi sama da rabin ƴan ƙasar kan mummunan yanayin zafi yayin da aƙalla mutane 18 ne suka mutu sakamakon zafin a ranar Litinin.

    A Birtaniya ma ana sa ran za a fuskanci mummunan yanayin zafi a tarihi a wannan watan na Yuni, inda yanayin zafi zai iya haura digiri 35 a ma’aunin Celsius.

    Haka kuma a Spain da Portugal, yanayin zafi ya wuce yadda aka saba gani a daidai irin wannan lokaci na shekara, inda wasu yankuna ke fuskantar ƙarin yanayin zafi mai tsanani.

  13. Dan majalisar Iran ya yi barazanar zaman dirshan kan rufe majalisa

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani dan majalisar dokokin Iran mai wakiltar Tehran, Kamran Ghazanfari, ya sanar da shirin gudanar da zanga-zanga a gaban majalisar kasar domin nuna adawa da rufe majalisar da aka yi na tsawon watanni.

    A wani sako da ya wallafa a shafin X, Ghazanfari ya ce wasu daga cikin ‘yan majalisa za su je ginin majalisar da karfe 8 na safe a ranar Lahadi.

    Ya ƙara da cewa idan har suka tarar majalisar a rufe, za su zauna a wajen a matsayin zaman dirshan har sai an sake buɗe ta.

    Dan majalisar ya bayyana kiran nasa ne ga al’ummar Iran, yana mai jaddada cewa rufe majalisar na dogon lokaci ba abin da ya dace ba ne.

  14. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Talata daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.