NAHCON ta kammala jigilar Alhazan Najeriya

Asalin hoton, Getty Images
Hukumar alhazai ta Najeriya NAHCON ta ce a hukumance ta kammala jigilar alhazan Najeriya sama da 38,000 da suka tafi ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2026.
Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar NAHCON, Hajiya Fatimah Usara ta fitar ta ce ana sa ran jirgin ƙarshe ɗauke da alhazai daga Jihar Zamfara zai iso Najeriya a ranar Talata.
Usara ta ce kammala jigilar ya kawo ƙarshen ayyukan Hajjin 2026.
Sai dai ta ce alhazan Najeriya 12 a halin yanzu suna jinya a asibitoci daban-daban na ƙasar Saudiyya saboda wasu matsalolin lafiya.
“NAHCON na bin diddigin halin da suke ciki, kuma ta shirya yadda za a dawo da su Najeriya lafiya da zarar an sallame su daga asibitoci.'' in ji ta
Usara ta ce, an ɗauki darassa masu ma’ana daga wannan aikin Hajjin bana, wanda za a yi amfani da su wajen inganta ayyukan Hajji da za su biyo baya.
Ta ce a bisa ƙudirin hukumar na ci gaba da inganta ayyukanta da kuma fara shiri tun da wuri, ta fara shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2027 a hukumance.
























