Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Yaƙin Iran, Amurka da Isra'ila da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya ta ranar Talata 20/5/2026.

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sauran sassan duniya ta ranar Laraba 20 ga watan Mayun 2026.

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Usman Minjibir da Nabeela Mukhtar Uba

  1. WHO na nazarin yiwuwar amfani da allurar rigakafin Ebola a DR Congo

    Hukumar lafiya ta duniya ta ce tana duba yiwuwar samar da allurar rigafi da maganin magance cutar Ebola domin taimakawa wajen shawo kan matsalar bazuwar cutar a Janhuriyyar Dimokradiyyar Kongo.

    A yanzu dai babu wata allurar rigakafin cutar da aka amince da ita a hukumance.

    Kwamitin bada agajin gaggawa na hukumar ya ce yana duba yiwuwar amfani da allurar rigakafi ta Ervebo da kuma allurar rigakafin da jami'ar Oxford ke ƙoƙarin samarwa nan da watanni uku masu zuwa.

    Anyi amannar cewa cutar ta kashe mutane dari da talatin da tara daga cikin dari shida da suka kamu.

    Shugaban hukumar lafiya ta duniya kenan Tedros Ghebreyesus yake cewa muna tsammanin adadin wadanda suka kamu da wadanda suka mutu zai ci gaba da ƙaruwa idan aka yi la'akari da yadda cutar ta bazu kafin a gano barkewar cutar.

  2. Jiragen ruwa 26 sun ratsa ta mashigar Hormuz cikin kwana ɗaya - Iran

    Rundunar juyin juya hali ta Iran ta ce ta bar jiragen ruwa 26 sun wuce ta mashigar hurmuz a cikin sa'o'i ashirin da hudu.

    Ta ce manyan tankokin mai da sauran jiragen ruwa na ƴan kasuwa sun wuce ta mashigar da taimakon dakarunta na ruwa.

    Daruruwan jiragen ruwa ne suka maƙale a mashigar yayin da ake ci gaba da nuna damuwa kan tasirin hakan a duniya.

    A ranar litinin ne Iran ta sanar da kafa hukumar kula da mashigar, da za ta riƙa daidaitawa da kula da cunkoso a mashigar.

    Jirgin Koriya ta Kudu da manyan tankokin China biyu na daga cikin waɗanda suka ratsa ta mashigar a yau.

  3. Za mu kai wa Iran hari idan ba ta amince da yarjejeniya ba - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce a ranar Laraba cewa tattaunawa da Iran ta shiga matakin ƙarshe, amma ya yi gargadin cewa za a iya kai sabbin hare-hare idan Tehran ba ta amince da yarjejeniya ba.

    Kimanin makonni shida bayan ya dakatar da kai hari kan Iran domin kafa yarjejeniyar tsagaita wuta, rahotanni na cewa tattaunawar kawo ƙarshen rikicin ba ta samu gagarumin ci gaba ba.

    Trump ya ce a wannan makon ya kusa bayar da umarnin ƙarin hare-hare, amma ya dakata domin bai wa tattaunawar ƙarin lokaci.

    “Mun shiga matakin ƙarshe na tattaunawa da Iran. Za mu ga abin da zai faru. Ko dai mu cimma yarjejeniya, ko kuma za mu yi abubuwan da ba su da daɗi, amma ina fata ba za a kai ga hakan ba,” in ji shi ga ‘yan jarida.

    Gwamnatin Iran ta mayar da martani da zargin cewa Trump na ƙoƙarin tayar da sabon yaƙi, tare da gargadin cewa idan aka kai wani hari, za ta mayar da martani har ma fiye da yankin Gabas ta Tsakiya.

  4. Indonesiya na shirin tsaurara dokar fitar da manja da gawayi zuwa ƙetare

    Shugaban ƙasar Indoneshiya Prabowo Subianto, ya ce zai tsaurara matakan hana fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen ƙetare, wadanda suka hada da manja da gawayi, matakin da ke shan suka daga masu samar da su.

    Ya ce ƙasarsa ta yi asarar kusan dala tiriliyan daya a cikin shekaru talatin, sakamakon sayar da kayan da rahusa ga kasashen ƙetare.

    Ya ce zai dauki matakin da ma'aikatun gwamnati ne kadai za su rika fitar da kayan.

    Indoneshiya ita ce ƙasar da ta fi kowace ƙasa a duniya samar da manja da yawanci ake amfani da shi a yankin Asiya da Afirka saboda saukin kudinshi

  5. Maƙiya na neman sake ƙaddamar da yaƙi - Iran

    Shugaban Majalisar Dokokin Iran, Mohammad Baqer Qalibaf, ya ce mostin da maƙiyan ƙasar ke yi a fili da kuma a ɓoye na nuna cewa har yanzu ba su yi watsi da manufofinsu na kai hare-hare a ƙasar ba, suna neman su ƙaddamar da yaƙi.

    Qalibaf ya bayyana haka ne a cikin saƙon murya na uku da ya fitar, inda ya yi nuni da cewa wata guda kenan da tsagaita wuta, yana mai cewa yanayin siyasar da ke kewaye da shugaban Amurka, Donald Trump, na da tasiri wajen yanke hukunci game da Iran.

    Ya ce ana ci gaba da matsin tattalin arziki da na siyasa kan Iran domin tilasta mata ja da baya, amma ya yi ikirarin cewa sojojin ƙasar sun yi amfani da wannan lokacin tsagaita wuta wajen sake gina ƙarfinsu da shirinsu na aiki.

    Shugaban majalisar ya kuma soki wasu ɓangarorin siyasa a cikin gida, yana zarginsu da yin watsi da yanayin tsaro tare da mayar da hankali sosai wajen sukar gwamnati. Ya ce irin waɗannan sukar na iya cutar da haɗin kan ƙasa.

  6. An bankaɗo 'gagarumar' masana'antar miyagun ƙwayoyi ta Najeriya da Mexico

    Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya NDLEA ta sanar da tarwatsa wata babbar ƙungiyar masu haɗa miyagun ƙwayoyi ta haɗin gwiwa tsakanin ƴan Najeriya da Mexico, bayan wani samame da jami’an hukumar suka kai a jihar Ogun da Legas.

    Hukumar ta ce ta kama shugaban ƙungiyar tare da wasu mutane ƴan asalin ƙasar Mexico uku da kuma mutum shida ƴan Najeriya, yayin da ta ƙwato sinadaran ƙera ƙwayar methamphetamine da darajarsu ta haura naira biliyan 480.

    Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa mai ritaya ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar hukumar da ke Abuja ranar Laraba.

    Ya ce bayan watanni ana tattara bayanan sirri ne jami’an sashen ayyuka na musamman suka kai samame cikin sa’o’i 48 a wasu wurare a Ogun da Legas.

    Ya bayyana cewa an gano wata babbar ma’aikatar ƙera muguwar ƙwayar meth a cikin dajin Abidagba da ke ƙaramar hukumar Ijebu East a Ogun, inda aka kama mutane bakwai ciki har da ƙwararrun masu ƙera ƙwayar daga ƙasar Mexico guda uku.

  7. An tauye wa Iran haƙƙin samar da man fetur da makamashi - Pezeshkian

    Shugaban ƙasan Iran, Masoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa ƙasar na fuskantar ƙuntatawa a samar da fetur da wasu nau’in makamashi, inda ya ce dole ne a sanar da ‘yan ƙasa gaskiyar halin da ake ciki domin samun fahimta da goyon baya.

    Ya bayyana cewa warware matsalar na buƙatar haɗin kai daga jama’a da kuma sauya yadda ake amfani da makamashi, tare da kira a samar da tsarin rabon fetur na jihohi bisa ainihin buƙatun kowace yanki.

    Rahotanni sun nuna cewa ana fama da matsalar rashin daidaito a fannin makamashi, inda amfani da fetur ya kai kusan lita miliyan 130 zuwa 135 a rana, yayin da samarwa kafin rikicin ke tsakanin lita miliyan 110 zuwa 115, sai kuma shigo da ƙarin lita miliyan 20 zuwa 25 a kullum.

    A gefe guda kuma, rahotanni sun ce hare-haren da suka shafi kayayyakin makamashi da matsin tattalin arziki sun ƙara dagula yanayin, yayin da takunkumin ruwan tekun Amurka ya rage damar shigo da kaya, lamarin da ke ƙara jefa tsarin makamashin ƙasar cikin matsin lamba.

  8. Babu sansanin ƴan ta'adda a Kudu maso Yammacin Najeriya - Sojoji

    Hedikwatar Tsaron Najeriya ta ce babu wata tabbatacciyar hujja da ke nuna cewa ’yan ta’adda sun kafa sansani na dindindin a yankin Kudu maso Yammacin ƙasar, duk da harin da aka kai a wasu makarantu a ƙaramar hukumar Oriire ta jihar Oyo.

    Babban hafsan tsaron ƙasa, Janar Olufemi Olatunbosun Oluyede, ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran tsaro, Manjo Janar Michael Onoja, ya fitar a jiya ranar 19 ga Mayun 2026.

    Janar Oluyede ya bayyana harin da aka kai makarantar Baptist da Community Grammar da kuma L.A. a matsayin mummunan aiki mara imani da ya girgiza zuƙatan ’yan Najeriya.

    Ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda abin ya shafa da gwamnatin jihar Oyo, tare da tabbatar da cewa rundunar sojin Najeriya za ta yi duk mai yiwuwa domin ceto mutanen da aka sace cikin aminci ba tare da wani sharaɗi ba.

    Sanarwar ta ce a baya sojoji sun gudanar da manyan ayyukan kawar da masu aikata laifi a dajin Old Oyo National Park, inda suka lalata ƙarfin masu aikata miyagun laifuka a yankin.

    Hedikwatar tsaron ta jaddada cewa binciken bayanan sirri da ake yi yanzu bai nuna akwai wata tsayayyar ƙungiyar ta’addanci da ta kafa sansani a dazukan yankin Kudu maso Yamma ba.

  9. Jirgin Koriya ta Kudu ya ratsa ta mashigar Hormuz tare da haɗin kan Iran

    Ministan harkokin wajen Koriya ta Kudu, Cho Hyun, ya ce a ranar Laraba wani jirgin tankar man ƙasar Koriya da ke ɗauke da ɗanyen mai ya ratsa ta mashigar Hormuz tare da haɗin kan hukumomin Iran.

    Sai dai bai bayar da ƙarin bayani game da jirgin ba yayin jawabinsa a wani zaman sauraron majalisa a birnin Seoul.

    Bayanan jigilar jirgin daga kamfanin LSAG sun nuna cewa babban tankar man mai suna Universal Winner mai ɗauke da tutar Koriya ta Kudu, wanda ke ɗauke da ganga miliyan biyu na ɗanyen man Kuwait, yana barin mashigar Hormuz.

    Ratsawar wannan tankar mai tare da haɗin kan hukumomin Iran na zuwa ne bayan da wani jirgin dakon kaya na Koriya mai suna HMM Namo ya fuskanci hari daga “jirage marasa matuƙa guda biyu da ba a san ko su wanene ba” a kusa da mashigar Hormuz kimanin makonni biyu da suka gabata, wato ranar 4 ga watan Mayu.

  10. China da Rasha sun soki ayyukan Amurka a Iran da Venezuela

    Rasha da China sun fitar da wata sanarwa ta haɗin gwiwa bayan tattaunawar shugabanninsu Vladimir Putin da Xi Jinping, inda suka nuna adawa ɓaro-ɓaro adawa da abin da suka kira “ayyukan sojin Amurka” a wasu sassan duniya kamar Iran da Venezuela.

    A cikin bayanin, ƙasashen biyu sun soki hare-haren bazata da amfani da tattaunawa a matsayin dabara kafin kai farmaki, da kuma abin da suka bayyana a matsayin ƙoƙarin sauya gwamnati da tayar da rikici a cikin ƙasashe masu zaman kansu.

    Sun kuma ce irin waɗannan matakai na tauye dokokin Majalisar Ɗinkin Duniya ne da tsarin duniya da aka kafa bayan Yaƙin Duniya na Biyu.

    Sanarwar ta kuma jaddada haɗin gwiwar makamashi tsakanin Moscow da Beijing, inda suka amince da zurfafa haɗin kai a fannin mai da gas da kwal.

    A batun Ukraine kuma, sun ce dole ne a magance abin da suka kira “tushen rikicin,” tare da kira ga bin ƙa’idar Majalisar Ɗinkin Duniya.

    Rahotanni na nuna cewa dangantakarsu da Amurka na ci gaba da zama cikin sarkakiya duk da tattaunawar diflomasiyya da ke gudana a baya-bayan nan.

  11. Sojoji sun daƙile harin ƴanbindiga a Arewa maso Gabashin Najeriya

    Rundunar Sojin Najeriya ta ce dakarun haɗin gwiwarta na Joint Task Force tare da Operation Hadin Kai sun samu nasarar daƙile wani hari mai ƙarfi da aka shirya kai wa a yankin Arewa maso Gabashin ƙasar, yayin ayyukan tsaro da suke gudanarwa a yankin.

    Rundunar ta ce sojojin nata sun kuma kama wasu da ake zargi da taimaka wa masu tayar da ƙayar baya da kuma ceto waɗanda aka yi garkuwa da su.

    A cewar sanarwar da rundunar ta fitar, harin da dakarun da ke sansanin FOB Gajibo suka daƙile, ana zargin cewa mayaƙan Boko Haram/ISWAP ne suka shirya kai harin inda suka taho da babura daga fannoni daban-daban.

    Sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa ta amfani da makamai masu nauyi, abin da ya tilasta wa maharan ja da baya.

    Rundunar ta ce sojojijin sun kuma ƙwace harsasai da wasu kayan yaƙi, ba tare da asarar rai a ɓangaren sojojin ba..

    Sanarwar ta kuma ce wani matashi ɗan shekara 17 da ke da alaƙa da iyalan ƴanbindigar ya tsere daga sansanin su da ke Dutsen Mandara, inda daga baya ya miƙa kansa ga sojoji a kan hanyar Gwoza zuwa Limankara.

  12. Minitsan harkokin cikin gida na Pakistan ya isa Iran kan tattaunawar zaman lafiya

    Ministan Harkokin Cikin Gida na Pakistan, Mohsin Naqvi ya isa birnin Tehran karo na biyu cikin ƙasa da mako guda, a ci gaba da tattaunawar diflomasiyya da ke gudana tsakanin Pakistan da Iran kan zaman lafiya a yankin.

    Pakistan ce ta taka rawa wajen shiga tsakani a tattaunawar da aka yi tsakanin Iran da Amurka a Islamabad, wadda ta ƙare ba tare da cimma matsaya ba.

    A makon da ya gabata, Naqvi ya bayyana a Tehran cewa ƙoƙarin ƙasarsa na neman zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin na iya haifar da sakamako mai kyau.

    A lokacin wannan ziyara, Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi ya shaida masa cewa “saɓani da kuma tsauraran matakan da Amurka ke ɗauka sune ke zama babban cikas ga hanyoyin diflomasiyya.”

  13. Masu takarar gwamna a APC sun ƙaurace wa zaɓen cikin gida a jihohi 10

    Gabanin zaɓen 2027, masu neman takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar APC sun ƙaurace wa tsarin zaɓen cikin gida a aƙalla jihohi 10, inda suka ƙi amince wa da matsin lamba na janyewa daga takara, suka dage cewa dole ne a ba su damar shiga zaɓe domin gwada karɓuwarsu a fili.

    Wannan rikicin ya taso duk da ƙoƙarin shugabannin jam’iyyar da gwamnoni a jihohi daban-daban na rage rikici ta hanyar amincewa da ‘yan takara guda ɗaya ko yin sulhu, domin kauce wa rabuwar kai gabanin babban zaɓe.

    Sai dai a jihohi irin su Kwara, Gombe, Oyo, Adamawa, Bauchi, Plateau, Lagos, Nasarawa, Rivers da Yobe, ana ci gaba da fafatawa mai tsanani.

    APC ta ƙayyade farashin fom ɗin neman takarar gwamna kan Naira miliyan 10, yayin da na tsayawa takara ya kai Naira miliyan 40.

    Rahotanni sun nuna cewa jam’iyyar ta samu kusan Naira biliyan 5.05 daga siyar da fom ga ‘yan takara 101 a faɗin ƙasar.

    Za a gudanar da zaɓen fidda gwani na jam'iyyar APC a jihohi 28 a ranar 21 ga Mayu, tare da amfani da zaɓe kai tsaye a wuraren da tsarin sulhu ya gaza.

    Ana kuma sa ran sauraron ƙorafe-ƙorafe a ranar 24 ga Mayu.

  14. An kashe ɗansanda da ke dab da ritaya a faɗan daba a Kano

    Wani jami’in ‘yan sanda da ke aiki a sashen Hotoro, wanda aka bayyana sunansa a matsyain Sani S.O ya mutu yayin wani faɗan ƙungiyoyin ‘yan daba a jihar Kano, watanni kaɗan kafin ya yi ritaya daga aiki kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    Rahotanni sun ce an tura jami’in tare da abokan aikinsa domin tarwatsa faɗan da ya ɓarke tsakanin ƴan daban, sai dai an ce wani daga cikinsu ya harbe shi da bindiga.

    Rahoton ya ce an garzaya da shi asibiti bayan harbin, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.

    An bayyana marigayin a matsayin jami’i mai nagarta da ya shafe fiye da shekaru 30 yana aiki a rundunar ‘yan sanda, kuma yana dab da ritaya cikin makonni kaɗan.

    A halin yanzu, rundunar ‘yan sandan jihar Kano ba ta fitar da cikakken bayani kan lamarin ba, yayin da ake ci gaba da fuskantar ƙaruwar rikice-rikicen ‘yan daba a sassa daban-daban na birnin Kano, ciki har da Hotoro da Fagge da Koki.

  15. Yaƙin Iran ya janyo rububin motoci na lantarki a duniya

    Hukumar kula da makamashi ta duniya ta ce yaƙin Iran ya janyo ƙaruwar sayen motoci masu amfani da lantarki a duniya da kusan kashi 28 cikin 100.

    Hukumar ta danganta wannan ƙaruwa da hauhawar farashin mai da ta biyo bayan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila.

    Rahoton ya ce tsadar mai ta sa mutane da dama sun koma amfani da motocin lantarki domin rage kashe kuɗin sufuri.

    A cewar hukumar, kusan ƙasashe 30 sun samu ƙarin masu sayen motocin da ke amfani da lantarki a watan Maris, ciki har da ƙasashen Latin Amurka inda aka samu ƙaruwa da kashi 75 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

    Rahoton ya kuma nuna cewa sauƙin farashin motoci na lantarki ya ƙara taimakawa wajen yawaitar sayensu a kasuwanni daban-daban.

    Sai dai rahoton ya nuna bambanci a Amurka, inda aka samu raguwar sayen motoci na lantarki a ƙarshen shekarar da ta gabata, duk da ci gaban da aka samu a wasu yankuna na duniya..

  16. Idan aka sake kai mana hari, yaƙi zai bazu fiye da yankin Gabas ta Tsakiya - Iran

    Rundunar Juyin Juya Halin Iran ta fitar da wata sanarwa da ke gargaɗin cewa idan Amurka da Isra’ila suka sake kai hari kan Iran, rikicin zai iya bazuwa fiye da yankin Gabas ta Tsakiya.

    A cikin sanarwar, rundunar ta mayar da martani ga barazanar sake kai hari da shugaban Amurka, Donald Trump, da wasu jami’an Isra’ila suka yi inda ta ce sake kai hari kan Iran zai haifar da faɗaɗa yaki zuwa sassa da dama na duniya.

    Ta ƙara da cewa duk wani farmaki zai fuskanci martani mai tsanani.

    A wani ɓangare kuma, ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya bayyana a shafinsa na X cewa Iran ta koyi darussa da yawa kuma ta ƙara ƙwarewa, yana mai cewa idan aka koma kai musu hari, to Amurka za ta ga abin mamaki.

    A gefe guda, shugaba Donald Trump ya ce a baya cewa ya dakatar da wani harin soji kan Iran a daidai lokacin da ake shirin aiwatar da shi, bayan roƙon wasu shugabannin yankin, lamarin da ke ƙara nuna yadda rikicin diflomasiyya da tsaro ke ci gaba da ɗaukar hankali a tsakanin ƙasashen biyu.

  17. Tsohon ministan sufuri Alƙali ya janye daga neman takarar gwamnan Gombe a APC

    Tsohon ministan sufuri kuma ɗan takarar gwamnan jihar Gombe a jam’iyyar APC, Sa'idu Ahmed Alkali, ya sanar da janye kansa daga shiga zaɓen fidda gwani na gwamna da jam’iyyar za ta gudanar ranar 21 ga watan Mayun 2026.

    A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Umar Alkali Jibrin ya fitar, Sanata Alƙali ya ce ya ɗauki matakin ne saboda abin da ya kira rashin gaskiya da karya dokokin zaɓe a jihar.

    Sanarwar ta bayyana cewa Alƙali ya cika dukkan sharuɗɗan shiga takarar gwamna, ciki har da sayen fom ɗin nuna sha’awa da na tsayawa takara tare da wuce tantancewar da jam’iyyar ta gudanar. Sai dai ya ce yadda aka gudanar da zaɓukan fidda gwani na majalisar wakilai da sanatoci a yankunan Gombe/Kwami/Funakaye, Billiri/Balanga da Gombe ta Tsakiya a ranakun 16 da 18 ga watan Mayu ya sa ya rasa ƙwarin gwiwa kan sahihancin tsarin zaɓen.

    A cewarsa, "zaɓukan sun gudana cikin maguɗi, rashin gaskiya da kuma karya sashe na 86 na dokar zaɓe ta 2026, wanda ya tanadi cewa dole ne a gudanar da zaɓen fidda gwani bisa ƙa’idojin jam’iyya."

    Ya ce an gudanar da zaɓukan ba tare da isassun kayan aiki da jami’an zaɓe da masu sa ido da sauran shirye-shiryen da suka dace ba, lamarin da ya nuna cewa babu adalci ko gaskiya a tsarin.

    Duk da janyewar tasa daga takarar, Sanata Alƙali ya tabbatar da ci gaba da biyayya da goyon bayansa ga jam’iyyar APC domin samun nasara a babban zaɓen shekarar 2027.

  18. Amurka za ta sha mamaki idan ta koma yaƙi da mu - Iran

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya mayar da martani ga kalaman barazanar shugaban Amurka, Donald Trump, dangane da yiwuwar sake kai hari kan Iran, inda ya ce: “Amurka za ta sha mamaki idan ta koma fagen yaƙi da mu.”

    Araghchi ya yi wannan gargaɗi ne a wani sabon saƙo da ya wallafa a shafin X inda ya ce

    “Watanni bayan fara yaƙin da aka yi da Iran, Majalisar Dokokin Amurka ta amince da lalata jirage masu yawa da darajarsu ta kai biliyoyin daloli. Yanzu kuma an tabbatar a hukumance cewa rundunar sojinmu mai ƙarfi ita ce ta farko a duniya da ta harbo shahararren jirgin yaƙin F-35 ta Amurka.”

    A ƙarshen saƙon nasa, ya yi iƙirarin cewa:

    “Da darussan da muka koya da kuma ilimin da muka samu, ku tabbatar cewa komawa fagen yaƙi zai kawo ƙarin abubuwan mamaki.”

    A jiya ne shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi iƙirarin cewa a daidai lokacin da ake shirin kai wani babban harin soji kan Iran, ya bayar da umarnin dakatar da harin bayan roƙon shugabannin yankin.

  19. Jiragen man China sun ratsa ta mashigar Hormuz bayan jinkirin fiye da wata biyu

    Wasu manyan jiragen dakon mai guda biyu na ƙasar China da ke ɗauke da ganga miliyan huɗu na ɗanyen mai sun ratsa ta mashigar Hormuz a ranar Laraba.

    Bayanan jigilar ruwa daga kamfanonin Kepler da LSGA sun nuna cewa manyan tankokin man guda biyun da ke ɗauke da ɗanyen man Gabas ta Tsakiya sun bar mashigar Hormuz bayan sun shafe sama da wata biyu suna jira a yankin Tekun Fasha.

    A cikin kwanakin baya-bayan nan, jiragen ruwa kaɗan ne kawai suka rika bi ta wannan muhimmiyar hanyar ruwa.

    Sai dai nasarar da jiragen suka samu wajen wucewa, tare da sauyin salon magana daga Fadar White House, ya sa farashin mai ya ɗan sauka kaɗan.

    A ranar Talata, shugaban Amurka, Donald Trump, ya jaddada cewa ana dab da cimma yarjejeniyar zaman lafiya da Iran, duk da cewa ya ce duk wata yarjejeniya da za a cimma dole ne ta hana Iran mallakar makamin nukiliya.

  20. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Laraba daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.