Ukraine na zargin Isra'ila da sayen ''hatsin sata'' daga yankunanta da Rasha ta mamaye
Ukraine ta gayyaci jakadan Isra'ila a ƙasar, bayan da Kyiv ta zargi Isra'ilar da sayen abin da ta kira hatsin sata daga yankunan Ukraine da Rasha ta mamaye.
Ministan harkokin wajen Ukraine Andrii Sybiha ya ce irin wannan sayayya na kawo cikas ga alaƙa mai kyau da ke tsakanin ƙasashen biyu.
Ya ce jirgin ruwan dakon kaya na biyu ya isa Haifa, bayan na farkon ya kai hatsi yakin.
Ministan harkokin wajen Isra'ila Gideon Sa'ar ya ce za a gudanar da bincike kan lamarin.
Sai dai kuma ya yi gargaɗin cewa zargi ba shaida bane, inda ya ja hankalinsu kan gudanar da hulɗar diflomasiyya ta intanet ko kafafen yaɗa labarai.




