KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 26/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo mu ku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Skip Bidiyo and continue reading
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Kutama
  • xxx
  • Sadis Buba

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. Amurka ta zargi Iran da kai hari kan wani jirgin ruwan dakon mai na Singapore

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Jami’an Amurka da ba a bayyana sunayensu ba sun shaidawa kafafen yaɗa labaran Amurka cewa sojojin ruwan Iran ne suka kai hari kan wata tankar mai da ke kusa da mashigar ruwan Hormuz a ranar Alhamis.

    Iran dai ba ta mayar da martani kan wannan zargin ba, amma rundunar sojin ruwa ta IRGC ta yi gargaɗi a daren Larabar da ta gabata cewa duk zirga-zirgar jirage ta mashigar Hormuz ba zai yiwu ba sai ta hanyoyin da aka sanar, kuma dole ne jiragen ruwa su bi ta mashigar tare da hadin gwiwar sojojin Iran.

    Gargadin na rundunar IRGC ya zo ne bayan da Oman ta sanar lokacin ziyarar da Marco Rubio ya kai a wasu ƙasashen yankin Gulf, cewa ta samar da wata sabuwar hanyar teku domin gaggauta tsallakawar jiragen ruwa ta mashigar Hormuz.

    Wannan labari dai ya samu karɓuwa daga Bahrain, amma bisa ga dukkan alamu sanarwar da rundunar sojojin ruwan ta IRGC ta yi wani martani ne mara kyau kan samar da wannan sabuwar hanyar.

    Sai dai har yanzu Iran ba ta amince ko musanta alhakin harin da aka kai kan jirgin ruwan na Singapore ba.

  2. Adadin waɗanda suka mutu a girgizar ƙasar Venezuela ya kai 235

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Masu aikin ceto na ci gaba da binciken ɓaraguzan gine-gine a Venezuela tyayin da su ke ƙoƙarin ceton rayuka bayan girgizar ƙasar da ta yi sanadin mutuwar mutane aƙalla 235.

    Rahotanni na cewa baya ga waɗanda suka mutu, aƙalla mutum 4,300 sun jikkata sakamakon girgizar ƙasar guda biyu masu karfin maki 7.2 da kuma 7.5 da ta suka afku da yammacin Laraba.

    A Caracas da La Guaira, ana jin mutane suna kiraye-kirayen neman taimako a ƙarƙashin ɓaraguzan gine-gine da suka ruguje.

    Shugaban majalisar dokokin Venezuela, Jorge Rodríguez, ya ce gine-gine 250 ne suka ruguje, akasarinsu a La Guaira, inda BBC ta tabbatar da hoton wani otal mai hawa 10 da ya koma ruguje har ƙasa.

    Har ila yau, an rasa gine-gine da dama a birnin ƙasar, in ji ministan harkokin cikin gida Diosdado Cabello. An kuma samu ɓarna sosai a Trujillo da Yaracuy da Carabobo da Aragua da kuma Miranda.

  3. Assalam Alaikum

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,Barkanmu da Safiya

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Kamar yadda aka sani za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.