Amurka ta zargi Iran da kai hari kan wani jirgin ruwan dakon mai na Singapore

Asalin hoton, Getty Images
Jami’an Amurka da ba a bayyana sunayensu ba sun shaidawa kafafen yaɗa labaran Amurka cewa sojojin ruwan Iran ne suka kai hari kan wata tankar mai da ke kusa da mashigar ruwan Hormuz a ranar Alhamis.
Iran dai ba ta mayar da martani kan wannan zargin ba, amma rundunar sojin ruwa ta IRGC ta yi gargaɗi a daren Larabar da ta gabata cewa duk zirga-zirgar jirage ta mashigar Hormuz ba zai yiwu ba sai ta hanyoyin da aka sanar, kuma dole ne jiragen ruwa su bi ta mashigar tare da hadin gwiwar sojojin Iran.
Gargadin na rundunar IRGC ya zo ne bayan da Oman ta sanar lokacin ziyarar da Marco Rubio ya kai a wasu ƙasashen yankin Gulf, cewa ta samar da wata sabuwar hanyar teku domin gaggauta tsallakawar jiragen ruwa ta mashigar Hormuz.
Wannan labari dai ya samu karɓuwa daga Bahrain, amma bisa ga dukkan alamu sanarwar da rundunar sojojin ruwan ta IRGC ta yi wani martani ne mara kyau kan samar da wannan sabuwar hanyar.
Sai dai har yanzu Iran ba ta amince ko musanta alhakin harin da aka kai kan jirgin ruwan na Singapore ba.















