Me ya janyo ambaliya a wasu sassan Abuja?

Asalin hoton, UGC
A ƙarshen makon nan ne wasu sassan Abuja, babban birnin Najeriya, suka fuskanci wata mummunar ambaliya da ta haddasa tsaikon zirga-zirga, lalata kadarori, tare da haifar da damuwa ga mazauna yankunan da abin ya shafa.
Lamarin ya sake jawo hankalin jama'a kan yadda birnin ke fama da matsalar ambaliya duk da kasancewarsa ɗaya daga cikin biranen da aka tsara bisa tanadin hukumomi.
Kodayake ruwan sama mai ƙarfi na daga cikin abubuwan da ke haddasa ambaliya, masana da dama na ganin matsalar ta wuce yawan ruwan sama.
Karanta abin da ya janyo ambaliyar daga bakin masana a hira da BBC































