Kotu ta tabbatar da David Mark a matsayin shugaban jam'iyyar ADC
A yau Alhamis, wata babbar kotun tarayya da ke zama a Abuja ta tabbatar da shugabancin jam'iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark.
Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar, bisa rashin hujjoji masu gamsarwa.
Da yake yanke hukunci, mai shari’a Musa Liman ya amince da buƙatun farko da jam’iyyar ADC da tsohon shugabanta Ralph Nwosu da Mark da sakataren jam’iyyar na ƙasa Rauf Aregbesola suka gabatar.
Alƙalin kotun ya ce kotun ba ta da hurumin sauraren ƙarar saboda lamari ne da ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa.
Alƙali Liman ya kuma yanke hukuncin cewa Abejide ba shi da hurumin shari'a na shigar da ƙarar, bayan ya kasa nuna yadda aka take masa haƙƙoƙinsa sakamakon fitowar shugabannin jam'iyyar ADC na yanzu.
Dangane da halascin bayyanar Mark da Aregbesola a matsayin shugabannin jam'iyyar, alƙali Liman ya ce sauyin shugabancin da aka samu daga Nwosu zuwa Mark bai saɓa wa kundin tsarin mulkin ADC ba.
Daga bisani, mai shari'a Liman ya yanke hukuncin cewa Abejide ya biya kowanne daga cikin waɗanda ake ƙara kuɗin da ya kai Naira miliyan 2.
Har ila yau, ya umurci lauyan Abejide da ya biya Naira miliyan 10 a matsayin kuɗaɗen shari'a, bisa tanade-tanaden Dokar zaɓe ta shekarar 2026.