KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 02/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Skip Bidiyo and continue reading
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Kutama
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. BBC ta gano wani mai safarar mutane da aka yanke wa hukunci a Faransa yana zaune a Birtaniya

    ...

    Wani bincike na BBC ya gano wani mai safarar mutane da aka yanke wa hukunci, wanda a da aka yi wa laƙabi da "ubangidan" sansanonin ƴan ci-rani na Faransa, yana zaune a Leicestershire kuma ana kyautata zaton yana neman mafaka yayin da yake aiki ba bisa ƙa'ida ba.

    An yanke wa Twana Jamal hukuncin ɗaurin shekara biyar a gidan yari a Faransa a shekarar 2016, inda hukumomi suka bayyana shi a matsayin ɗaya daga cikin manyan masu safarar mutane da aka taba kamawa.

    Masu gabatar da ƙara sun ce ɗan Iraƙin, mai shekara 36 a lokacin, ya samu har zuwa £100,000 a mako guda saboda jigilar bakin haure ba bisa ƙa'ida ba zuwa ƙasashen Turai.

    Bayan samun wasu bayanai a kansa a cikin wannan shekarar, mun gano Jamal a ƙauyen Blaby kuma mun samu shaida yana aiki, yana tuƙa mota ba tare da lasisi ba kuma da alama yana amfani da sunan ƙarya.

    Kasancewar Jamal a Burtaniya ta haifar da damuwa sosai game da ko hukumomin kan iyaka da ke akwai suna da tasiri wajen gano masu neman mafaka waɗanda suka aikata manyan laifuka a ƙasashen waje.

  2. Aƙalla mutum 13 sun mutu bayan harin da Rasha ta ƙai babban birnin Ukraine

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Jami'ai sun ce dakarun Rasha sun kai wani mummunan harin makami mai linzami a babban birnin Ukraine Kyiv cikin dare, inda suka kashe aƙalla mutum 13.

    An kwashe mutane da dama daga gidajensu yayin da hare-haren suka girgiza gine-gine a faɗin birnin, sa'o'i bayan da shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya yi gargaɗin cewa Rasha na shirin kai wani babban hari.

    Rahotanni na cewa yara na cikin akasarin waɗanda suka mutu, in ji Tymur Tkachenko, shugaban gwamnatin soji ta Kyiv.

    "Maƙiyan mu suna sake kai hari kan ungwannin mutane da gangan suna kashe fararen hula," in ji shi da sanyin safiyar Alhamis.

    Ma'aikatar Tsaro ta Rasha ta yi iƙirarin cewa ta kai hari kan cibiyoyin makamashi ne saboda hare-haren da Ukraine ta kai kwanan nan.

  3. Assalamu Alaikum!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Alhamis daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda muke kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.