KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 8/08/2026

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Asabar 8 ga watan Agustan 2026.

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. Trump ya soki kotun Amurka bisa dakatar da gini dala miliyan 400 a White House

    Donald

    Asalin hoton, EPA

    Donald Trump ya yi kakkausan maartani ga hukuncin da kotun daukaka kara ta Amurka ta yanke na dakatar da gina dakin taro na dala miliyan dari hudu a Fadar White House.

    Mista Trump ya ce hukuncin siyasa ce kawai kuma abin kunya ne ga kasa Wakilin BBC ya ce hkuncin kotun wani cikas ne ga matakin Trump na gina dakin taron Mr Trump ya ce zai daukaka kara zuwa Kotun Koli.

    A bara ne, Mista Trump ya rusa wani bangare na Fadar White House domin samar da wurin shirya taro. Kotun ta ce irin wannan gagarumin aiki ya kamata ya sami amincewar Majalisa.

  2. Harin mayaƙan Houthi ya kashe aƙalla 10 a Yemen

    Houthi

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani harin mayakan Houthi ya kashe akalla mutum 10 a birnin Marib na Yamen.

    Mayakan masu samun goyon bayan Iran da kuma ke rike da ikon babban birnin Yemen har zuwa yammacin Marib sun ce sun kai harin ne kan dakarun da ke samun goyon bayan Saudiyya.

    Sun kai harin ne kwana guda bayan kashe wasu dakarun gwamnatin Yemen da dama a wani hari ta sama da mayakan na Houthi suka kai a sasanonin soji na Marib da lardin Hadramawt bayan mutuwar wasu fararen hula 11 a wani harin na Houthi a yankin Najran na Saudiyya

  3. Amurka da Isra'ila ba su ci ribar yaƙi da mu ba - Iran

    Iran

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    A cikin wata sanarwa da rundunar dakarun juyin-juya-halin Iran (IRGC) ta fitar a yayin bikin ranar ƴan jarida, rundunar ta ce Amurka da Isra’ila ba su cimma manufofinsu ba a yaƙe-yaƙen baya-bayan nan da suka yi da Iran.

    Ta ce abin da ta kira “yarjejeniyoyin da aka cimma” ba komai ba ne illa “takardar miƙa wuya da Amurka ta yi ga halin da ake ciki a fagen daga da kuma ƙarfin Iran wajen tattaunawa.”

    Sanarwar ta kuma ce Washington ta fuskanci “tsaka mai wuya ta fuskar dabarun yaƙi” a yaƙin da take yi da Iran, sannan kuma an samu ɓaraka tsakanin ƙawayenta na ƙasashen Yamma.

    Sai dai IRGC ba ta bayyana takamaiman yarjejeniyoyin da take magana a kansu ba.

  4. Farawa

    Jama'a masu bibiyar wannan shafi na kai-tsaye daga BBC Hausa.

    A wannan shafi za mu ci gaba da kawo muku labaran abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na Facebook da X da kuma Whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.