Duk wani katsalandan ga ikon ƙasarmu a mashigar Hormuz zai ƙara tsananta rikici ne - Iran

Asalin hoton, Getty Images
Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, ya yi gargaɗin cewa duk wani yunƙuri na katsalandan a yadda Iran ke tafiyar da mashigar Hormuz zai ƙara tsananta rikici a yankin.
Araqchi, wanda ke ziyara a birnin Baghdad, ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai tare da takwaransa na Iraq, inda ya ce bisa fahimtar juna tsakanin Iran da Amurka, za a dawo da zirga-zirgar mashigar cikin kwanaki 30, a ƙarƙashin cikakken ikon Iran kaɗai.
Ya jaddada cewa Iran ce ke da alhakin aiwatar da wannan tsari, yana mai cewa duk wani ƙoƙari na ƙirƙirar wata hanya dabam ko tsoma baki daga waje zai janyo tsaiko da kuma ƙarin rikice-rikice, wanda a cewarsa tuni an fara gani a abubuwan da suka faru cikin dare biyu a yankin.
A cikin kwanaki uku da suka gabata, an kai hari kan aƙalla jiragen ruwa biyu da ke wucewa mashigar Hormuz, lamarin da ya haddasa musayar wuta tsakanin Iran da Amurka, inda kowanne ɓangare ke zargin ɗaya da karya yarjejeniyar tsagaita wuta..


















