KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, 09/05/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, 09/05/2026

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Jirgin sama buge wani mutum a Amurka

    jirgin sama na Frontier

    Asalin hoton, Getty Images

    Fiye da fasinjoji 200 aka fitar daga wani jirgin sama a Amurka bayan da ya jirgin ya bugi wani mutum da ke tafiya a kan titin jirgin kafin tashinsa.

    Direban jirgin ya dakatar da shirin tashi bayan faruwar lamarin, sakamakon wutar da ta kama ɗaya daga cikin injunan jirgin.

    A wani saƙon murya da aka naɗa daga ɗakin kula da tashin jiragen an ji muryar direban jirgin na cewa injin jirgi ya kama da wuta.

    Kamfanin jirgin, Frontier, da ya mallaki jirgin ya ce ya kaɗu da faruwar lamarin, kuma tuni aka ƙaddamar da bincike.

  2. Starmer na fuskantar matsin lamba bayan jam'iyyarsa ta sha kaye a zaɓen Birtaniya

    Starmer

    Asalin hoton, PA Media

    Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, na ci gaba da fuskantar matsin lamba daga cikin jam'iyyarsa ta Labour kan ya sauka daga muƙaminsa, sakamakon shan kaye da jam'iyyar ta yi a zaɓukan ƙananan hukumomi da kansiloli a faɗin ƙasar a jiya Alhamis.

    A zaɓen ƙananan hukumomi a Ingila - dukkanin manyan jam'iyyun ƙasar biyu - Labour - mai mulki da kuma Conservative mai hamayya - sun yi rashin nasara sosai - galibi a hannun jam'iyyar Reform UK - mai ra'ayin riƙau.

    Haka kuma jam'iyyar ta Labour ta sha gagarumin kaye a zaɓukan majalisar dokokin yankin Wales.

    Can ma a yankin Scotland jam'iyyar National Party ce ta yi nasarar cin kujerun majalisar dokokin yankin fiye da kowace jam'iyya - kodayake ba ta samu rinjayen da take buƙata ba.

    Ƴan majalisar dokokin Labour fiye da 20 ne suka fito fili suna kiran ya sauka ko kuma ya sanya wani lokaci da zai ajiye muƙamin.

    To sai dai Mista Starmer ya yi watsi da kiran nasu, yana mai cewa ba zai sauka ba, inda ya alƙawarta shawo kan matsalolin da al'ummar ƙasar ke nuna damuwa a kansu.

  3. Amurka za ta shirya gagarumar tattaunawa tsakanin Isra'ila da Lebanon

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Amurka ta tabbatar cewa za ta shirya babbar tattaunawa ta tsawon kwana biyu tsakanin Isra'ila da Lebanon ranar Alhamis da Juma'a na mako mai zuwa.

    Ta ce ɓangarorin biyu za su tattauna ainun a kan samar da cikakkiyar yarjejeniyar zaman lafiya da tsaro.

    Har yanzu dai a hukumance akwai ƙwarya-ƙwaryar yarjejeniyar zaman lafiya a tsakaninsu.

    To amma jami'an Lebanon sun ce hare-haren da Isra'ila ke kai wa a kudancin Lebanon ɗin sun hallaka mutum bakwai a jiya Juma'a kaɗai.

    Ita ma ƙungiyar Hezbollah da ke samun goyon bayan Iran ta ce ta ƙaddamar da hare-haren makamai masu linzami da na ƙananan jiragen sama marasa matuƙa a kan sansanonin sojin Isra'ila, domin ramuwar gayya a kan harin da Isra'ila ta kai Beirut ranar Laraba - wanda ya kashe daya daga cikin manyan kwamandojinta.

  4. An ga alamar malalar mai a tsibirin Kharg na Iran

    Hotunan tauraron ɗan'adam sun nuna wata malalar mai da ta kai ta faɗin murabba'in kilomita 50 a kusa da Tsibirin Kharg - babbar cibiyar samar da mai ta Iran.

    Ba a dai san takamaiman me ya haddasa malalar ba, da aka gani a gaɓar yamma ta tsibirin.

    Wata ƙungiya da ba ta gwamnati ba - mai lura da batutuwan rikici da kuma muhalli - The Conflict and Environment Observatory - ta ce alamu sun nuna cewa malalar ta yi kama da ta mai, kuma tana kwaranya ne zuwa kudanci.

    Tsibirin Kharg, nan ne Iran take da yawancin rijiyoyin mai da bututan man da tankunan ajiya da dai sauran kayayyaki na harkar manta.

  5. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye, barkanmu da safiyar wannan rana ta Asabar.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku domin kawo muku halin da duniyar ke ciki.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.