KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 30/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 30 ga watan Yunin 2026.

Skip Bidiyo and continue reading
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Kutama
  • xxx
  • Sadis Buba

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Ba mu shirya wata tattaunawa da Amurka a Doha ba - Iran

    ....

    Asalin hoton, Tasnim news agency

    Iran ta musanta iƙirarin Trump cewa za a fara sabbin tattaunawa da Amurka a Doha, tana mai cewa ba ta shirya wata ganawa ko tattaunawa da Amurka ba a wannan lokaci ba.

    Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta ce wakilan ƙasar da ke tafiya Doha ba don tattaunawa ba ne, sai dai domin bibiyar batun kuɗaɗen ƙasar da aka ƙwace a ƙasashen waje.

    Wannan matsaya na Tehran ya zo ne duk da cewa Trump ya bayyana cewa za a gudanar da ganawa tsakanin wakilan ƙasashen biyu a babban birnin Qatar.

    Sai dai jami’an Iran sun musanta wannan batu, suna jaddada cewa babu wani shiri na ganawa ko tattaunawa da suka shirya yi da Amurka a kwanaki masu zuwa.

    A wani ɓangare, Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya ce kimanin dala biliyan 6 daga cikin biliyan 12 na kuɗaɗen Iran da aka ƙwace za su sake dawowa da su hannun gwamnati nan ba da jimawa ba.

    Ya ce ana ci gaba da bin matakan da suka dace domin ganin an saki kuɗaɗen, wanda ake ganin zai taimaka wajen karfafa tattalin arzikin ƙasar.

    Haka kuma, Iran ta yi martani ga bayanan da shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi, inda ta jaddada cewa ita kaɗai ce ke da ikon gudanar harkokin mashigin Hormuz.

  2. An fara zanga-zangar ƙyamar baƙi a Afrika ta Kudu bayan cikar wa'adi

    ...

    An fara zanga‑zangar ƙyamar baƙi a sassa daban‑daban na Afirka ta Kudu, lamarin da ya sa aka jibge jami’an tsaro saboda fargabar rikice‑rikice.

    Shugaba Cyril Ramaphosa ya buƙaci masu zanga‑zangar su guji tashin hankali, yana mai jaddada cewa dole ne a gudanar da zanga‑zanga cikin lumana ba tare da tsoratarwa ba.

    Zanga‑zangar na da alaƙa da wa’adin da wasu ƙungiyoyi suka bai wa baƙin da ba su da takardu su fice daga ƙasar.

    Hakan ya sa mutane da dama suka fara tserewa saboda tsoron hare‑hare, yayin da hukumomi suka ce an riga an mayar da sama da mutum 25,000 kasashensu, yawancinsu daga wasu ƙasashen Afirka.

    ...

    A birnin Johannesburg, inda ake gudanar da wasu daga cikin zanga‑zangar, an samu tsaiko a harkokin yau da kullum, inda shaguna da dama suka rufe, kuma aka samu yanayi na tsoro da shiru.

    Dubban baƙi kuma na cigaba da jiran a kwashe su a sansanonin wucin gadi domin tsira da lafiyarsu.

    ....

    A gefe guda, Shugaba Ramaphosa ya tunasar da jama’a cewa baƙin da ke zaune bisa doka na da haƙƙi kamar kowa, yana mai cewa suna taka muhimmiyar rawa wajen gina tattalin arziƙin ƙasar.

    A Durban kuwa, ana rushe sansanonin da ke ɗauke da ‘yan Malawi, yayin da wasu ke bayyana takaicinsu na barin iyalansu da rayuwar da suka fara ginawa sakamakon matsin lamba da matsalar tsaro.

    ...
    ....