KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 04/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai kai-tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 04/06/2026.

Skip Bidiyo and continue reading
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Sadis Buba
  • Pantami
  • xxx
  • Nafiu Gombe
  • Mace da ƴarta mai lalaurar Autism
  • wata mata
  • BBC reporter

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, Haruna Kakangi

  1. Ƴansanda sun ƙaryata rahoton sakin ɗaliban Oyo

    ...

    Asalin hoton, @OyoPoliceNG/X

    Rundunar ƴansanda a jihar Oyo ta musanta rahotannin da ake yaɗawa a shafukan sada zumunta inda ake zargin cewa ƴanbindiga suk sako ɗalibai da malaman da suka sace a ƙaramar hukumar Orire a jihar Oyo.

    Rundunar ta bayyana haka a sanarwar da kakakinta, DSP Ayanlade Olayinka ya sanyawa hannu inda ta ce rahoton ƙarya ce tsagwaranta.

    Cikin sanarwar, rundunar ta kuma bai wa al'ummar jihar ta Oyo tabbaci cewa ana ci gaba da ƙoƙari na ganin an kuɓutar da ɗaliban da malaman.

    Rundunar ta kuma yi kira ga mazauna jihar da su guji jita-jita su kuma nemi sahihan labarai daga ƴansanda.

    Lamarin hare-haren 'yan bindiga da satar mutane don neman kuɗin fansa sun fi ƙamari ne a yankin arewacin Najeriya, inda ba kasafai aka saba ganin hakan ba a kudancin ƙasar, wadda ke fama da matsaloli na tsaro.

    A baya-bayan nan ita ma dai jihar ta Oyo na fuskantar matsalar tsaron daga gungun masu aikata laifi.

  2. An yi musayar wuta kan rikicin zaɓe a Somaliya

    ....

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Dakarun gwamnati da mayaƙa sun yi musayar wuta a Mogadishu, babban birnin Somaliya sakamakon rikici game da jan ƙafa wajen gudanar da zaɓe.

    Wa'adin Shugaba Hassan Sheikh Mohamud kan karagar mulki ya zo ƙarshe ranar 15 ga watan Mayu amma an tsawaita shi da shekara ɗaya.

    Ɓangaren hamayya ya ce hakan ya saɓa da kundin tsarin mulki inda kuma suka kira a gudanar da zanga-zanga a yau Alhamis.

    Rahotanni sun ce an ji ƙarar harbe-harbe a wasu yankuna na babban birnin har zuwa cikin dare, kamar yadda mazauna yankin suka bayyana.

    Ƴansanda sun ce suna aiwatar da gagarumin samame ne kan mayaƙa masu riƙe da makamai da suka kai hare-hare a yankunan.

    Bayan cikar wa'adin shugaban ƙasar ne gwamnatin tarayya da ɓangaren hamayya suka shiga tattaunawa sai dai sun gaza cimma matsaya.

  3. An kashe Falasɗinawa 11 a hare-haren Isra'ila

    Jami'an lafiya da shaidu a Gaza sun ce an kashe Falasɗinawa aƙalla 11 inda wasu da dama suka ji rauni a hare-haren da Isra'ila ta kai a ranar Alhamis.

    Likitoci sun shaida wa BBC cewa wani jirgin Isra'ila ya kai hari kan aƙalla gidaje huɗu a birnin Gaza.

    Daga cikin waɗanda rahotanni ke cewa harin ya shafa akwai wani kwamandan Hamas wanda aka kashe tare da mai ɗakinsa da kuma ƴaƴansa uku.

    Isra'ila ta kai hare-hare a Gaza duk da yarjejeniyar tsagaita wuta ta watan Oktoba da Amurka ta shiga tsakani, inda take zargin Hamas da sake haɓaka sojojinta.

    Fiye da mutum 940 aka kashe tun lokacin, a cewar ma'aikatar lafiyar Falasɗinu.

  4. Ƴanbindiga sun sace ɗaliban kwalejin fasaha a Zamfara

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar ƴansanda a Najeriya ta ce ƴanbindiga sun sace wasu ɗaliban kwalejin fasaha ta tarayya da ke Ƙaura Namoda a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin ƙasar.

    An sace ɗaliban bakwai da sanyin safiyar jiya Laraba daga gidan da suka zaune a wajen yankin.

    Kakakin rundunar ƴansandan jihar Yazid Abubakar cikin wata sanarwa ya ce maharan sun kutsa gidajen ɗaliban inda kuma suka yi awon gaba da wasu daga cikinsu.

    Sanarwar ta ƙara da cewa an tuntuɓi sojoji da jami'an da aka tura yankin sai dai ƴanbindigar sun riga sun tsere kafin jami'an tsaro su isa wajen.

    "Ɗaya daga cikin ɗaliban da aka sace ya samu tserewa kuma tuni aka miƙa shi ga hukumomi yayin da ake ƙara ƙoƙari na gano ragowar mutum shida," in ji sanarwar.

    Rahotanni sun ce jami'an tsaro tuni suka fara samame domin gano inda ƴanbindigar suke kuma zuwa yanzu babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai harin.

    Jihar Zamfara da Kebbi da Katsina masu maƙwabtaka na fuskantar ƙaruwar hare-hare a baya-bayan nan sakamakon ayyukan ƴanbindiga.

  5. Gwamnatin Najeriya na son masu sola su riƙa sayar mata da lantarki

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar kula da wutar lantarki a Najeriya NERC ta fara amfani da wani tsari wanda zai bai wa masu amfani da sola damar siyar wa hukumomi lantarki.

    NERC ta bayyana haka ne a shafinta na X inda ta ce "idan sola ɗinku na samar da lantarki fiye da buƙatarku, za ku iya sayar wa kamfanonin rarraba lantarki ƙarin wuta kuma a biya ku kuɗi"

    A cewar NERC, wannan tsarin shi ake kira Prosumer a Turancin Ingilishi wato inda kwastoma zai kasance mai amfani da kuma samar da lantarki.

    Sai dai akwai ƙa'idoji da ke tattare da tsarin da suka haɗa da dole ka zama kwastoma a kamfanin rarraba lantarki sannan kuma dole sola ɗin da mutum ya saka ta zama mai ƙarfin 50kwp.

    Kazalika, dole sai mutum ya samu izini daga kamfanin rarraba lantarki bugu da ƙari kuma sai ka sa hannu kan yarjejeniya ta sabon tsarin sannan kuma mutum sai ya yi rajista da NERC.

    Sanarwar ta ce tsarin bai shafi gidaje masu amfani da matsakaicin sola ba.

  6. Isra'ila da Lebanon sun yarda su aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta

    ..

    Asalin hoton, Reuters

    Isra'ila da Lebanon sun amince da sabunta ƙwarya ƙwaryar yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma ƙirƙirar wasu yankuna na tsaro na gwaji - inda sojojin Lebanon za su karɓi iko da su.

    Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa ta haɗin gwiwa daga ɓangarorin biyu bayan tattaunawa da Amurka da ta shiga tsakani a Washington.

    Wakiliyar BBC ta ce ɓangarorin biyu sun ce sabuwar yarjejeniyar ta dogara ne akan dakatar da buɗe wuta da Hezbollah ke yi gaba daya da kuma kawo ƙarshen dukkan ayyukansu a yankunan da ke kudancin Lebanon.

    Tuni dai Hezbollah da ke samun goyon bayan Iran ta yi watsi da matakin.

  7. Majalisar dokokin Amurka ta buƙaci Trump ya daina yaƙi a Iran...

    Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar wakilai ta Amurka ta kaɗa ƙuri'a inda ta umarci Shugaba Donald Trump ya janye sojojin Amurka daga yakin Iran, ko kuma ya nemi amincewar majalisun dokokin ƙasar kan ci gaba da yaƙin.

    Ƴan majalisar daga jam'iyyar Republican huɗu sun goyi bayan ƴan Democrats wajen amincewa da wannan mataki wanda yanzu zai wuce zuwa majalisar dattawan ƙasar.

    Matakin da aka ɗauka dai ya kasance na je-ka na yi-ka ne a yayin da shugaban ƙasa ke da ikon hawa kujerar na-ƙi a kan duk wani hukunci ko matakin da ya ga zai ka wo masa matsala a shugabancinsa.

    Wannan shi ne matakin na baya-bayan nan na kara nuna adawa da matakin Trump din a kan Iran, daga cikin jam'iyyarsa ta Republican.

  8. Barka da warhaka!

    Barka da zuwa shafin BBC Hausa na kai-tsaye wanda ke kawo muku labaran duk abubuwan da ke faruwa game da yaƙin Iran da kuma muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da saurarn sassan duniya a wannan rana ta Alhamis - ta-bawa, ranar samu.

    Za ku iya yin tsokaci a shafukanmun na sada zumunta: facebook, X, instagram, YouTube sai kuma zaurenmu na WhatssApp.