Abubuwan da ke faruwa kan yaƙin Iran da Amurka da sauran batutuwa, Litinin 13/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Litinin 13/07/2026

Taƙaitattu

Skip Bidiyo and continue reading
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza da Muslim Muhammad Yusuf

  1. Atiku ya buƙaci magoya bayan ADC su kwantar da hankalinsu bayan hukuncin kotu

    Atiku Abubakar

    Asalin hoton, Atiku/X

    Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya buƙaci mambobin jam'iyyar ADC da sauran ƴan Najeriya su kwantar da hankalinsu bayan hukuncin klotun ɗaukaka ƙara kan shugabancin jam'iyyar.

    A cikin wata sanarwa da kakakinsa, Phrank Shaibu, ya fitar, Atiku ya ce saɓanin yadda wasu ke yaɗawa, hukuncin kotun bai soke zaɓen fidda gwani da jam'iyyar ADC ta gudanar domin tsayar da ƴan takararta a zaɓen 2027 ba.

    Ya ce "abin da wasu ke yaɗawa cewa hukuncin ya kawo ƙarshen takarar shugaban ƙasa ta ADC wani yunƙuri ne na yaɗa bayanan da ba su dace ba domin raunana ƴan adawa da kuma ruɗar da ƴan Najeriya."

    Atiku ya bayyana cewa hukuncin kotun ya shafi zaɓen shugabannin jam'iyyar a matakin ƙananan hukumomi ne da kuma wa'adin shugabannin kwamitocin riƙo na jihohi, ba zaɓen fidda gwani na tsayar da ƴan takara ba.

    Atiku ya ce su na girmama hukuncin kotun, amma sun umarci lauyoyinsu da su ɗaukaka ƙara zuwa kotun ƙoli domin ta yanke hukunci na ƙarshe kan lamarin.

    Ya kuma buƙaci magoya bayan ADC kada su karaya, inda ya ce "gwagwarmayar ceto Najeriya ba ta za ta ta'allaka kan hukuncin kotu guda ɗaya ba"

  2. Amurka ta ce za ta ci gaba da toshe mashigar ruwan Iran daga ranar Talata

    Jirgin ruwan Iran

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Amurka mai kula da yankin Gabas ta Tsakiya (CENTCOM) ta sanar cewa za ta ci gaba da toshe zirga-zirgar jiragen ruwa da ke fitowa daga tashoshin jiragen ruwa na Iran daga ranar Talata.

    A wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, CENTCOM ta ce matakin zai fara aiki ne daga ranar Talata, inda zai shafi duk jiragen ruwa da ke zuwa ko fitowa daga tashoshin jiragen ruwa da yankunan gabar tekun Iran.

    Sai dai rundunar ta ce za ta ci gaba da tabbatar da zirga-zirgar sauran jiragen ruwa cikin aminci a yankin, muddin ba su karya dokokin takunkumin ba.

    Dama shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa gwamnatinsa za ta sake ƙaƙaba wannan takunkumi kan zirga-zirgar jiragen ruwa masu hulɗa da Iran.

    A cewar CENTCOM, sabon matakin zai biyo bayan irin takunkumin da Amurka ta aiwatar tsakanin 13 ga Afrilu zuwa 18 ga Yuni.

    Sanarwar ta zo ne bayan Iran ta sanar da rufe Mashigar Hormuz har sai abin da hali ya yi, sakamakon sabon rikicin da ya ɓarke tsakanin ƙasar da Amurka.

  3. Ina da yaƙinin cewa Mojtaba Khamenei ba ya raye — Trump

    Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce yana da yaƙinin cewa Mojtaba Khamenei, ɗan marigayi Ayatollah Ali Khamenei, ya mutu, yana mai cewa akwai yiwuwar hakan da kashi 90 cikin 100.

    Trump ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da ya yi da gidan talabijin na Fox News, inda ya ce, "Khamenei ya mutu, kuma yarda da kashi 90 cikin 100 cewa ɗansa ma ya ɓace."

    Tun bayan yaƙin da aka yi, ba a sake ganin Mojtaba Khamenei a bainar jama'a ba, kuma ba a fitar da wani sabon hoto, ko saƙon murya ko bidiyonsa ba.

    Ko da yake kwanaki biyu da suka gabata an wallafa wani hoto a shafin intanet na jagoran Iran, babu wata shaida da ke nuna cewa hoton na kwanan nan ne.

    Trump ya kuma sake jaddada ikirarinsa cewa an lalata rundunar sojin ruwa da ta sama ta Iran, tare da tsarin kariyar ƙasar, sannan ya ce an kashe manyan kwamandojinsu.

    A yayin tattaunawar, shugaban na Amurka ya ce an cimma matsaya kan nukiliyar Iran bayan wata ganawa da ta ɗauki sa'o'i 11, sai dai bai bayyana cikakken bayani kan taron ba.

    Ya kuma zargi Iran da yaudarar shugabannin Amurka tsawon shekaru 47 da suka gabata, ciki har da Bill Clinton, George W. Bush da Barack Obama, yana mai cewa Obama shi ne "mafi muni" a cikinsu.

  4. Hukuncin kotu bai shafi ƴan takarar da muka tsayar ba — ADC

    ADC Logo

    Asalin hoton, ADC Vanguard/X

    Jam’iyyar adawa ta ADC a Najeriya ta ce hukuncin da kotun ɗaukaka ƙara ta yanke kan zaɓukan shugabannin jam’iyyar a jihohi bai shafi ƴan takarar da ta tsayar domin shiga zaɓe ba.

    Jam’iyyar ta bayyana cewa hukuncin kotun ya shafi batun zaɓen shugabannin jam’iyya daga matakin gunduma zuwa ƙananan hukumomi da jihohi ne kawai, ba zaɓen fidda gwani da aka yi na fitar da ƴan takararta ba.

    Sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar jim kaɗan bayan sanar da hukuncin kotun.

    Abdullahi ya ce hukuncin ba shi da wani tasiri kan ƴan takarar da jam’iyyar ta tsayar a dukkan matakai, inda ya yi kira ga mambobi da magoya bayan jam’iyyar da su kwantar da hankalinsu.

    “Hukuncin kotun ko kaɗan bai shafi zaɓen fidda gwani da jam’iyyarmu ta gudanar ba,” in ji shi.

    Jam’iyyar ta kuma bayyana cewa ta fara shirin ɗaukaka ƙara kan hukuncin, saboda ba ta amince da shi ba, domin a cewarta hakan bai yi daidai da doka ba.

    “Muna kira ga dukkan mambobin jam’iyyar da miliyoyin magoya bayanmu da su kwantar da hankalinsu, cikin ƙwarin gwiwa,” in ji sanarwar.

    Jam’iyyar ta ce za ta ci gaba da bin hanyoyin doka domin kare matsayinta, tare da tabbatar da burinta na samar da wata dama ga ƴan Najeriya.

  5. Kotu ta soke zaɓukan shugabannin ADC na jihohi

    ADC

    Asalin hoton, Atiku/X

    Kotun ɗaukaka ƙara a Abuja ta tabbatar da hukuncin da ya hana shugabancin riƙon ƙwarya na jam'iyyar ADC ƙarƙashin jagorancin Sanata David Mark gudanar da zaɓukan shugabannin jam'iyyar a jihohi.

    Kotun ƙarƙashin mai shari'a Abba Mohammed ta amince da hukuncin babbar kotun tarayya da mai shari'a Joyce Abdulmalik ta yanke a ranar 29 ga Afrilu, wanda ya hana hukumar zaɓe ta ƙasar INEC amincewa ko sa ido kan duk wani zaɓen shugabanni jam'iyyar da kwamitocin riƙon ƙwarya da shugabancin David Mark suka shirya.

    A hukuncin da mai sharia Okong Abang ya karanto, wanda alƙalai biyu suka amince ɗaya ya ƙi amicewa, kotun ta tabbatar da hukuncin da ya hana shugabancin David Mark tsoma baki cikin wa'adin mulki shugabannin jam'iyyar da aka zaɓa a jihohi.

    Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, kotun ta ce gudanar da zaɓukan shugabannin jam'iyya a matakin jiha haƙƙin shugabannin jihohin da aka zaɓa ne, ba shugabancin ƙasa ba.

    Sai dai mai shari'a Abba Mohammed da bai amince da matakin ba, ya ce babbar kotun tarayya ba ta da hurumin sauraron ƙarar tun da Kotun Ƙoli ta riga ta bayyana cewa rikice-rikicen cikin gida na jam'iyyun siyasa batu ne da ya shafi jam'iyya, ba kotu ba.

  6. Komai na tuna min da mahaifina - Zahra Buhari

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo

    Ɗiyar marigayi Muhammadu Buhari, Zahra ta ce kewarsa da suke yi ba za ta misaltu ba.

    Kazalika, Sheikh Qaribullah Kabara ya ce marigayin na ba wa malamai dama su yi masa nasiha a lokacin mulkinsa.

  7. Birtaniya ta sanya dakarun juyin juya halin Iran cikin ƙungiyoyin ta'adda

    Dakarun juyin juya hali

    Asalin hoton, ATTA KENARE/AFP/Getty Images

    Gwamnatin Birtaniya ta bayyana cewa ta saka rundunar juyin juya halin Iran cikin jerin ƙungiyoyin da ta haramta.

    Matakin wanda ke nufin saka rundunar ta IRG cikin jerin ƙungiyar ta'addanci na duniya, ya jima ana tattauna shi a Birtaniya.

    A baya wasu ƴanmajalisa da ƴansiyasar Birtnaiya sun riƙa yin kiraye-kirayen hakan.

    Gwamnatin Birtaniyar ta ɗauki matakin ne bayan wasu hare-hare da aka kai wa Yahudawan Birtaniya, inda majalisar ƙasar ta amince da dokar tsaron ƙasa, wadda a baya firaminista Kier Starmer ya alƙawarta.

    A baya, dokokin haramta ƙungiyoyi a matsayin ƴanta'adda ba ya haɗa wa da ƙungiyoyi da gwamnatoci ke goyon baya.

    Sabuwar dokar ta ƙunshi haramta taimaka wa IRGC ko yin kalamai da ke goyon bayan aƙidar rundunar.

  8. Yemen ta kai hari filin jirgin Sanaa don hana jirgin Iran sauka

    jirgin

    Asalin hoton, Reuters

    Gwamnatin Yemen da ƙasashen duniya ta amince da ita ta ce dakarunta sun kai hari kan titin saukar jiragen sama na filin jirgin saman Sanaa, domin hana wani jirgin saman Iran sauka.

    Sai dai ƙungiyar Houthi, wadda ke iko da birnin ta zargi Saudiyya da kai hare-hare ta sama kan filin jirgin, tare da gargaɗin cewa za ta ɗanɗana kuɗarta.

    Saudiyya na goyon bayan gwamnatin ƙasar yayin da Iran ke mara wa ƙungiyar Houthis baya.

    Wani jirgin dakon mai ya ce wasu ƙananan kwale-kwale sun tunkare shi a gaɓar tekun kudancin Yemen.

    Sai dai har yanzu ba a bayyana cikakken abin da ya faru ba, amma a baya ƙungiyar Houthis ta sha tare jiragen ruwa a wannan yanki.

  9. Sojojin Najeriya sun ce sun gano ƴan ƙasashen waje cikin mayaƙan ISWAP

    Rundunar sojin Najeriya ta ce ta gano wasu ƴan ƙasashen waje uku cikin mayaƙan ISWAP da suke taimaka wa ƙungiyar kitsa hare-harenta a Najeriya.

    Cikin wata sanarwa da rundunar Operation haɗin kai mai yaƙi da Boko Haram da ISWAP a arewa maso gabashin Najeriya ta fitar, ta ce ta gano mutanen uku ne cikin na'urar ɗaukar hoton mayaƙan ƙungiyar da suka ƙwato a wani gumurzu da mayaƙan yankin Cross Kauwa na jihar Borno

    Sojojin Najeriyar sun ce sun gano wani Balasɗine mai suna Abu Ishaq da suka ce shi ne babban mai horas da mayaƙan ƙungiyar.

    Sai kuma Abu, Thaiba da sojojin suka bayyana da likitan ƙungiyar, da kuma wani mutum da suka ce suna ƙokarin gano ƙasarsa da sunansa da kuma aikin da yake yi wa ƙungiyar ba.

    Da ma dai an jima ana zargin hannun ƴankasashen waje a ayyukan ƙungiyoyin ISWAP da Boko Haram.

    Sanarwar ta ce a lokacin fafatawa da mayaƙan ƙungiyar ɗaya daga cikin amsu ɗaukar wa ƙungiyar hotuna ne ya jefar da kyamarar wadda ta ƙunshi hotuna da bayanan yadda mayaƙan suka kitsa shirya hari kan sansanonin soji.

  10. Iran ta musanta iƙirarin Trump na cimma yarjejeniya kan nukiliyarta

    Abbas Araghchi

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma'aikatar harkokin wajen Iran ta musanta iƙirarin Shugaba Trump na Amurka kan cimma yarjejeniya ganme da nukiliyarta.

    A ranar Lahadi ne Shugaba Trump ya faɗa wa kafar yaɗa larabai ta NBC cewa Iran ta amince ta cimma yarjejeniya da Amurka game da nukiliyarta a wata tattaunawa tsakanin ƙasashen biyu.

    "Sun cimma yarjejeniya mai kyau da mu a jiya, babu batun nukiliya ba wani abu makamancin hakan, sun haƙura da komai,'' in ji Trump.

    To sai dai kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran ya ce iƙirarin na Trump ba gaskiya ba ne.

    Masu shiga tsakani na ci gaba da ƙoƙarin sansanta tsakanin Amurka da Iran.

  11. Fiye da mutum 2,700 sun mutu saboda zafin rana a Ingila da Wales

    Wani bincike ya bayyana cewa sama da mutum 2,700 , sun mutu sakamakon tsananin zafin da aka fuskanta a Ingila da Wales a tsakanin watan Mayu da Yunin da suka wuce.

    Masu bincike daga Jami'ar Imperial College da ke Landan, da Hukumar Kula da Yanayi ta Birtaniya da kuma Makarantar Koyar da kula da lafiyar al'umma ta London sun ce yanayin zafi da sauyin yanayi sun taka muhimmiyar rawa wajen yawan mutuwar mutanen.

    Rahoton ya ce mafi yawan mace-macen, sun faru ne a lokacin da aka fuskanci tsananin zafi a watan Yuni, wato lokacin da girman zafin da ya kai digiri 37.7 a ma'aunin Celsius.

    Masu binciken sun ce tsananin zafin ya ƙara nuna irin tasirin da sauyin yanayi ke da shi ga lafiyar dan adam. break

  12. Gwamnatin Najeriya ta dakatar da shirin ƙara kuɗin WAEC da NECO

    Dalibai

    Asalin hoton, Waec/X

    Gwamnatin Najeriya ta dakatar da shirin ƙara kuɗin jarrabawar WAEC da NECO ga ɗaliban sakandire ta ƙasar.

    Cikin wata sanarwa da ma'aikatar ilimin ƙasar ta fitar, ta ce an dakatar da shirin ne domin sake shawara game da shi da kuma tuntuɓar masu ruwa da tsaki.

    Tun da farko ma'aikatar ta ce za ta ƙara yawan kuɗin jarrabawar biyu daga naira 27,000 zuwa 50,000 daga shekarar 2027 mai kamawa.

    Ma'aikatar ilimin ta bayyana dalilai na tattalin arziki, inda ta ce a halin tattalin arzikin da ake ciki 27,000 ba zai iya biyan buƙatun jarrabawa ba.

    Matakin ya haifar da suka da muhawara daga ƴanƙasar da dama, waɗanda ke ganin shirin zai ƙara yawan kuɗin jarrabawar zai ƙara yawan ɗaliban da za su daina zuwa makaranta.

    Inda aka riƙa kiraye-kiraye ga gwamnati da ta jingine shirin nata.

    Ma'aikatar ta ce ta yaba wa shawarwarin da ta samu kan batun daga ƴanƙasar.

  13. An yanke wa shugaban RSF hukuncin ɗaurin rai da rai a Sudan

    Hemedti

    Asalin hoton, Anadolu via Getty Images

    Wata kotu a jihar Port Sudan, da ke ƙasar Sudan ta yanke wa jagoran RSF, Mohamed Hamdan Dagalo, da aka fi sani da ''Hemedti", hukuncin ɗaurin rairai da rai.

    A wata shari'a da aka yi a bayan Hemedti, wanda bai halarci kotun ba, an same shi da laifin aikata kisan ƙare dangi da laifukan yaƙi da laifukan jin ƙai da kuma hare-hare kan fararen hula.

    Hukuncin kotun da aka yanke ranar Lahadi 12 ga watan Yulin 2026, shi ne mafi girma da aka yi wa jagoran na RSF tun bayan fara yaƙin a 2023.

    Shari'ar ta mayar da hankali ne kisan da aka yi w gwamnan Yammacin Darfur, Khamis Abbakar, a shekarar 2023.

    An zargin garkuwa da shi sannan aka kashe shi bayan da ya zargi dakarun RSF da aika kisan ƙare dangi.

    Hukuncin ya kuma haɗa da wasu manyan jami'ar RSF, ciki har da ƴan'uwan Hemedti, Abdelrahim Dagalo da Algoney Dagalo, duk a bayan idonsu.

  14. Mun kai hare-hare kan sansanonin sojin Amurka a Bahrain da Kuwait - Iran

    Ana kai hare-hare

    Asalin hoton, EPA/Shutterstock

    Rundunar juyin juya halin Iran ta ce ta kai hari kan wata cibiyar kula da jiragen yaƙin Amurka da ke Bahrain.

    Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, IRGC ta ce ta kai hare-hare kan cibiyar gyaran jirage masu saukar ungulu da jiragen yaƙi na P-8 da kuma cibiyar kula da jirage marasa matuƙa da ke sansanin sojojin Amurka na Sheikh Issa da ke Bahrain.

    Haka kuma rundunar juyin juya halin ta ce ta kai hari kan tankokin mai da ke sansanin sojin saman Amurka na Prince Hassan da ke ƙasar Jordan.

    ''Haka kuma mun kai hari kan na'urorin tsaron samaniya da ke sansanin Ali Salem a ƙasar Kuwait da kum sansanin sojin sama na Ahmed Al-Jaber.

    Zaman ɗarɗar tsakanin Iran da Amurka kan iko da mashigar Hormuz na ci gaba da ƙaruwa a ƴankwanakin nan.

  15. Amurka na da damar ƙwace mashigar Hormuz - CENTCOM

    CENTCOM

    Asalin hoton, US CENTCOM

    Tsohon babban kwamandan rundunar sojin Amurka mai aiki da Gabas ta Tsakiya, CENTCOM, Janar Frank McKenzie (mai ritaya) ya ce sojojin Amurka na da ƙarfin da za su ƙwace iko da mashigar Hormuz, idan shugaban Amurka ya ga damar yin hakan.

    Cikin wata hira da kafar yaɗa labarai ta CBS, tsohon janar ɗin ya ce samun iko da mashigar Hormuz na buƙatar aika jiragen ruwan Amurka, yana mai cewa ''sojojin ruwan Amurka ba su ga damar yin hakan ba ne, amma suna da ƙarfin hakan''.

    Msita McKenzie na kalaman ne a matsayin martani da iƙirarin da iran ta yi cewa ta rufe mashigar Hormuz tare da kai hare-hare kan jiragen ƴan kasuwa.

    Toshon Janar ya kuma bayar da shawawar ƙwace iko da tsibirin Kharg domin samun damar tattaunawa da Iran don ta buɗe mashigar ta Hormuz.

  16. Farashin mai ya fara tashi bayan musayar wutar Amurka da Iran

    Farashin ɗanyen mai ya fara ƙaruwa bayan shafe kwanaki ana musayar wuta tsakanin Amurka da Iran, da kuma samun saɓanin bayanai kan halin da ake ciki a mashigar Hormuz.

    Farashin ɗanyen mai ya ƙaru da kusan kashi uku cikin ɗari, yayin da kasuwannin hannayen jari a sassan Asiya suka fara faduwa.

    Taƙaddamar da ake yi kan iko da mashigar Hormuz ta daƙile yunƙurin da ake na kawo ƙarshen rikicin da ake tsakanin ɓangarorin biyu.

    Rundunar sojin Amurka ta ce ta kai hare-hare kan wurare da dama a cikin dare, da nufin rage ƙarfin Iran na kai hare-hare kan jiragen ruwa na kasuwanci da ke bi ta mashigar Hormuz.

    A nata ɓangaren, rundunar juyin juya halin Musulunci ta Iran, ta ce ta mayar da martani ta hanyar kai hare-hare kan sansanonin sojojin Amurka da ke Jordan da Bahrain da kuma Kuwait.

  17. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa barkanmu da safiyar wannan rana ta Litinin, Mande tushen aiki ko da nasara na tsoroki, kamar yadda Hausa ke yi mata kirari.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku irin wainar da ake toyawa a faɗin duniya.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.