Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Gasar Kofin Duniya 2026 da sauran labaran wasannin BBC Hausa na wannan mako

Wannan shafi ne da ke kawo mu ku labaran Gasar Kofin Duniya 2026 da sauran labaran wasannin BBC Hausa na wannan mako 6-12 ga watan Yulin 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. Amorim ya nemi afuwar magoya bayan Man United

    Ruben Amorim ya nemi afuwa saboda rashin yin magana da magoya bayan Manchester United tun bayan korarsa da aka yi a watan Janairu, amma ya ce yana "alfahari" da kasancewa kocinsu.

    Amorim ya yi tsit da bakinsa tun bayan barin Old Trafford kuma ya zaɓi kin yin duk wani bayani game da watanni 14 da ya yi a Old Trafford a shafukan sada zumunta.

    Kocin mai shekaru 41 yanzu ya kawo ƙarshen hutunsa daga wasa ta hanyar sanya hannu kan kwantiragin shekaru uku da AC Milan.

    An gabatar da Amorim a ranar Laraba a babbar ƙungiyar ta Serie A - amma a wani taron manema labarai na mintuna 35 ba a nemi ya yi magana game da lokacinsa a United ba har sai da tambaya ta ƙarshe.

    A lokacin, tsohon kocin Sporting ya riga ya amince cewa ya yi wasu kurakurai a United kuma yana matuƙar sha'awar samun nasara saboda yadda "aikinsa na ƙarshe" ya kasance.

    Lokacin da aka tambaye shi ko waɗanne kura-kurai ya ke nufi, Amorim bai amsa tambayar kai-tsaye ba amma ya bayyana nadamarsa ga magoya bayan United saboda rashin magana da su.

  2. Ƙungiyar London City ta ɗauki Alexia Putellas

    Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta London City Lionesses ta sanya hannu kan yarjejeniyar shekaru uku da Alexia Putellas, wadda ta lashe kyautar Ballon d'Or sau biyu, a wani lamari da ya zama ɗaya daga cikin ciniki mafi ban mamaki a fagen wasan ƙwallon ƙafar mata.

    Ana yi wa ƴar wasan tsakiyar ta Spain Putellas kallon ɗaya daga cikin manyan ƴan wasa, ta bar Barcelona bayan shekaru 14 a watan Mayu kuma ya jawo hankalin kusan dukkan manyan ƙungiyoyin ƙwallon ƙafan mata a duniya.

    Ƴan wasan mai shekaru 32 ta lashe kofuna 38 tare da Barcelona, ​​ciki har da kofuna 10 na lig ɗin Spain.

    An gabatar da ita a birnin New York tare da mai hamshaƙiyar mamallakiyar ƙungiyar ta London City Michele Kang.

  3. Kocin Croatia ya yi murabus bayan jagorantar tawagar ƙasar na shekara tara

    Zlatko Dalic ya yi murabus bayan shekaru tara a matsayin kocin Croatia bayan shan kaye a hannun Portugal a gasar cin kofin duniya.

    Kocin mai shekaru 59 ya karɓi ragamar horas da tawagar ƙasar a shekarar 2017 kuma ya jagoranci Croatia zuwa wasan ƙarshe na gasar cin kofin duniya ta 2018 da kuma matsayi na uku shekaru huɗu bayan haka.

    Ƙasar Croatia ta fice daga gasar cin kofin Turai ta 2020 da aka jinkirta a zagaye na 16 kuma ta kasa kai wa matakin kifa-ɗaya-ƙwala na gasar Euro 2024, duk da cewa sun zo na biyu a gasar cin kofin ƙasashen Turai (Nations League) ta 2023.

    "Bayan kusan shekaru tara, babban koci Zlatko Dalic ya yanke shawarar rufe babinsa mai matuƙar nasara tare da Croatia," in ji wata sanarwa daga hukumar ƙwallon ƙafa ta Croatia.

  4. Hukumar ƙwallon ƙafar Masar ta shigar da ƙara kan alƙalan wasanta da Argentina

    Hukumar ƙwallon ƙafa ta Masar ta ce ta yi kira ga FIFA da ta kori alƙalan wasan da suka yi aiki a wasan da ta yi rashin nasara a hannun Argentina a gasar cin kofin duniya a zagaye na ƴan 16.

    Hukumar ta ce ta shigar da ƙara ga hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya kuma tana son a gudanar da bincike kan abin da ta bayyana a matsayin "rashin daidaito" a yadda aka yi alƙalanci wasan.

    Mataimakin alƙalin wasa na bidiyo (VAR) ya soke ƙwallo na biyu da Mostafa Zico ya ci saboda ƙeta da ɗan wasan tsakiya Marwan Attia ya yi wa Lisandro Martinez kafin aka ci ƙwallon.

    Kuma sun dage cewa an yi wa Mohamed Salah ƙeta ƴan daƙiƙa kaɗan kafin Argentina ta farke ƙwallo na biyu.

  5. Switzerland ta kai zagayen kwata fainal bayan doke Colombia a bugun fenariti

    Switzerland ta tsallake zuwa zagayen daf da na kusa da na ƙarshe na gasar cin kofin duniya a karon farko tun 1954 bayan ta doke Colombia a bugun fenariti a ranar Talata a zagaye na ƴan 16.

    Wasan ya ƙare 0-0 bayan mintuna 120, amma Switzerland ta yi nasara da ci 4-3 a bugun fenarirti, kuma yanzu za ta fafata da Argentina a daren Asabar a Kansas City.

    Davinson Sanchez ne ya ɓarar wa Colombia fenariti na biyu, kuma Switzerland ta yi amfani da damar, bayan Cucho Hernandez ɓarar da fenaritin Colombia na huɗu. Ruben Vargas ya zura Fenarirtin Swtzerland na ƙarshe da ya bai wa ƙasarsa nasara.

  6. Ɗan wasan Aston Villa Amadou Onana ya ji mummunan rauni a gwiwarsa

    Ɗan wasan tsakiya na Aston Villa Amadou Onana ya ji mummunan rauni a gwiwarsa ta dama a lokacin da yake bugawa Belgium wasa a gasar cin kofin duniya.

    An maye gurbin ɗan wasan mai shekaru 24 a minti 21 a wasan da tawagar ƙasarsa ta doke Amurka da ci 4-1 a zagaye na ƴan 16 na ƙarshe.

    Onana ya riƙe da gwiwarsa ta dama yayin da suke rige-rigen kai wa ga ƙwallon da shi da Christian Pulisic.

    Bayan an yi masa jinya a filin wasa, daga baya an gan shi a riƙe sanduna kuma yana sanye da takalmin gyaran gwiwa.

    A cikin wata sanarwa, likitan tawagar Belgium Brahim Hacene ya ce "rauni ne mai muni".

    Belgium ta ce Onana zai ci gaba da kasancewa tare da tawagar don karawar da za su yi da Spain a matakin daf da na kusa da na ƙarshe a Los Angeles ranar Juma'a.

    Irin wannan raunin yawanci yana sa ƴan wasa su yi jinya na tsawon wata shida zuwa tara.

  7. Arsenal na shirin ɗaukar Meslier kan cinikin kyauta bayan barinsa Leeds United

    Arsenal ta kusa kammala cinikin ɗaukar mai tsaron gida Illan Meslier a kyauta daga Leeds.

    BBC Sport ita ce ta farko da ta bayyana sha'awar Gunners kan Meslier a ranar 30 ga Yuni kuma yanzu an cimma yarjejeniya.

    Meslier da wakilansa sun kasance a cibiyar horas da kulob ɗin da ke Hertfordshire don kammala cikakkun bayanai game da cinikin kuma a yi masa gwajin lafiya a ranar Talata.

    Ɗan wasan mai shekara 26, wanda ya rasa matsayinsa na lamba ɗaya a Leeds, kwantiraginsa zai ƙare a wannan bazarar kuma don haka zai zo ne kan kyauta.

    Akwai shakku kan makomar mai tsaron gida na yanzu Kepa Arrizabalaga a kakar wasa mai zuwa, wanda hakan zai sa Arsenal ta fara neman wanda zai maye gurbinsa.

    A halin da ake ciki yanzu dai, Meslier zai zo ne a matsayin mai tsaron gida na uku a bayan David Raya da Arrizabalaga.

  8. Za a hana ƴan wasan Ingila tsallaka allunan talla

    Za a shawarci 'yan wasan Ingila da su guji tsallake allunan talla bayan da Jordan Henderson ya samu rauni jim kaɗan bayan nasarar da suka samu kan Mexico a gasar cin kofin duniya.

    Ana sa ran za a yi wa ɗan wasan tsakiya na Brentford Henderson tiyata a kan raunin da ya samu a wuyan hannunsa yayin murnar nasarar da Ingila ta samu da ci 3-2 a filin wasa na Azteca.

    Wannan yana nufin cewa akwai babban shakku game yiwuwar fafatawarsa a sauran wasannin gasar.

    An fahimci cewa koci Thomas Tuchel na shirin umartar ƴan wasansa da su guji tsallake allunan talla domin tabbatar da cewa hakan bai sake faruwa ba.

    Wani ɗan tawagar likitocin Ingila ya raka Henderson inda ya ci gaba da zama a asibitin da ke Mexico City a yammacin ranar Lahadi, kuma bai dawo tare da sauran ƴan tawagar zuwa sansaninsu da ke Kansas City ba.

  9. Iraola ya kama aikin horas da Liverpool a hukumance

    Sabon kocin Liverpool Andoni Iraola ya isa cibiyar horaswar ƙungiyar ta AXA , inda yawancin ƴan wasa da ma'aikatan ƙungiyar za su koma Merseyside a mako mai zuwa a ranar 14 ga Yuli.

    Wannan zai bai wa ɗan ƙasar Spain ɗin fiye da wata guda tare da tawagarsa kafin wasan farko na Premier League da Liverpool za ta kara da Newcastle a ranar 23 ga watan Agusta.

    To yaya zai kasance ga Iraola da Liverpool a wata mai zuwa?

    Daya daga cikin abubuwan farko da za su faru shine nazarin ƴan wasan da suka dawo kafin fara aikin tukuru.

    Babban abin da za a mayar da hankali a kai shi ne salon wasan ƙwallon ƙafa mai zafi da saurin gaske, kuma babu makawa za a sami sauye-sauye, a ɓangaren tawagar masu horaswa.

    Iraola zai yi aiki tare da Tommy Elphick da Shaun Cooper - waɗanda suka kasance tare da shi a Bournemouth - a matsayin masu horar da ƙungiyar farko.

  10. Akwai yiwuwar Rasha za ta iya shiga gasar Olympics ta 2028

    Za a iya ba wa ƴan wasan Rasha damar shiga gasar Olympics ta 2028 a Los Angeles bayan da kwamitin wasannin Olympics na duniya ya ɗage dakatarwar da aka yi musu na wucin gadi.

    Hukumar ta IOC ta dakatar da kwamitin wasannin Olympics na Rasha a shekarar 2023 a matsayin martani ga yaƙin da ake yi a Ukraine.

    Amma ya ce an dakatar da haramcin kuma ƴan wasa daga Rasha za su iya sake yin gasa muddin suka "cika ƙa'idojin hana shan magungunan ƙara kuzari".

    Har yanzu ba a yanke shawara kan ko Rasha za ta iya nuna tutarta da launukanta da kuma takenta a wasannin Olympics ba.

    IOC ta ce ba za ta ci gaba da "da ƙin shirya taron na IOC a Rasha ko kuma gayyatar jami'an gwamnatin Rasha zuwa abubuwan da hukumar ta shirya".

    Wasu ƴan wasan Rasha sun shiga gasar Olympics ta Paris ta shekarar 2024 da kuma gasar Olympics hunturu ta shekarar nan a Milan a matsayin masu zaman kansu.

  11. Martinez ya yi murabus daga muƙaminsa na kocin Portugal

    Roberto Martinez ya tabbatar da cewa zai ajiye aikin koci bayan da Portugal ta fice daga gasar cin kofin duniya a zagaye na ƴan 16 a hannun Spain.

    Ɗan ƙasar Spain mai shekaru 52 ya ga tawagarsa ta sha kashi da ci 1-0 a wasan da aka buga a filin wasan Dallas Cowboys da ke jihar Texas.

    Rashin nasarar da portugal ta yi ya sa ɗaya daga cikin manyan ƴan wasan ƙwallon ƙafa zai yi ritaya ba tare da ya lashe babbar ƙyautar wasan ta duniya ba,bayan da wasan ƙarshe na gasar cin kofin duniya na Cristiano Ronaldo da Portugal ya ƙare da shan kashi a hannun Spain da ci 1-0 a zagaye na ƴan 16.

    Ronaldo ya fashe da kuka yayin da labarinsa na gasar cin kofin duniya ya ƙare a Dallas inda Mikel Merino ya zura ƙwallon da ya tabbatar da ficewar Ronaldo da tawagarsa.

    Wanda ya lashe gasar zakarun Turai sau biyar kuma zakaran gasar Euro 2016 ya zura ƙwallaye 976 a duk wasannin da ya bugawa ƙungoyoyinsa da kuma tawagar ƙasarsa.

    Ya zura ƙwallaye a gasar cin kofin duniya sau shida. Amma mafi kusancin da ya taɓa yi da lashe gasar shine lokacin da Portugal ta kai wasan kusa da na ƙarshe a gasarsa ta farko a 2006.

    Ya riga ya sanar da cewa wannan zai zama gasar cin kofin duniya ta ƙarshe - amma daga baya ya ce "Zan haɗu da iyalina kuma in yanke shawara cikin natsuwa" lokacin da aka tambaye shi ko zai ci gaba da bugawa ƙasarsa wasa.

    Amma tambayar da aka kasa amsawa ita ce ko da Portugal za ta sami damar lashe wannan gasar cin kofin duniya da kocin bai fuskanci matsin lambar farawa da Ronaldo a kowane wasa ba?

  12. Cacar baki ta kaure tsakanin Mbappe da wata ƴar majalisar Paraguay

    Ɗan wasan gaba na ƙasar Faransa Kylian Mbappe ya yi alla-wadai da wata ƴar majalisar dattawan ƙasar Paraguay ya kuma bayyana ta a matsayin wadda ba ta cancanci matsayinta ba bayan da ta yi kalaman nuna wariyar launin fata da izgilanci ga asalinsa da kuma iliminsa.

    Celeste Amarilla, ƴar jam'iyyar Liberal Radical Party ta Paraguay, ta wallafa kalamn na ta ne a shafinta na dandalin X bayan da ƙasarta ta sha kashi a hannun Faransa a zagaye na yan 16 a gasar cin kofin duniya.

    Mbappe ya mayar da martani inda ya ce: “Madame Celeste Amarilla, ke mace ce mara mutunci kuma ba ki cancanci matsayinki ba. "Ba ki wakiltar Paraguay, ƙasar da ta nuna karamci da jajircewa a lokacin wanna gasar.

    Hukumar ƙwallon ƙafa ta Faransa (FFF) ta sanar da shirin gurfanar da Amarilla a gaban kotu, inda ta bayyana kalamanta a matsayin abin "kyama".

    Gwamnatin Paraguay ta bayyana cewa tana "yin alla-wadai da kuma ƙin amincewa da kalaman" da Amarilla ya yi, inda ta ce sun "saɓa wa ɗabi'u da ƙa'idojin da ke karfafa zaman lafiya da mutunta mutuncin ɗan adam, waɗanda kasarmu ke ingantawa."

    Kalaman na Amarilla sun zo ne bayan na tsohon mai tsaron ragar Paraguay, Jose Luis Chilavert, wanda kafin a fara wasan ya ce tawagar ƙasarsa za ta fafata ne da "kungiya daga Afirka".

  13. Ana sa ran James zai dawo a wasan daf da na kusa da na ƙarshe da Norway

    Ana sa ran Reece James zai dawo domin taka leda a wasan daf da na kusa da na ƙarshe da Ingila za ta fafata da Norway.

    Matsalar rashin ɗan wasan baya na hannun dama da Tuchel ke fuskanta ta ƙara tsananta bayan an bai wa Jarell Quansah jan kati a wasan da suka doke Mexico da ci 3-2 ranar Lahadi.

    Hakan na nufin ɗan wasan bayan na Bayer Leverkusen ba zai buga wasan gaba da tawagar Ingila za ta yi a Miami ba.

    James bai koma cikakken atisaye ba tukuna sakamakon raunin da ya samu a tsokar cinyarsa yayin wasansu na biyu a matakin rukuni da suka buga da Ghana, kuma bai samu buga wasannin suka yi da Panama da DR Congo da Mexico ba.

  14. Firaminista ya shiga tsakani kan taƙaddama kan lokacin fara wasan Mexico da Ingila

    Firaminista da sakataren harkokin waje sun shiga cikin jayayya kan cewa kada a dawo da lokacin fara wasan Ingila da Mexico baya - kamar yadda Fifa ta yi nazarin yin hakan ƴan kwanaki kafin wasan.

    Sir Keir Starmer ya umurci jami'ai tare da haɗin gwiwar Hukumar Kwallon Kafa ta ƙasar da su gabatar da hujjoji — cewa ya kamata a bar wasan a lokacin da aka tsara shi tun farko, kamar yadda jaridar The Sun ta ruwaito.

    Yvette Cooper ta tattauna da jakadan Birtaniya a Mexico domin neman jami'an diflomasiyyar Birtaniya su nuna rashin amincewarsu da duk wani sauyi, ta yadda magoya bayan tawagar Ingila su 3,000 da suka yi tafiya zuwa wurin ba za su rasa damar kallon wasan ba sakamakon hakan.

    An dai shirya Fifa za ta dawo da wasan baya da sa'o'i shida, saboda hasashen tsawa da aka yi.

    A ƙarshe dai, Fifa ta tsaya kan lokacin da aka shirya farawa, amma sai aka jinkirta wasan da awa ɗaya saboda rashin kyawun yanayi.

  15. Za a yi wa Henderson tiyata a hannu bayan raunin da ya ji

    Ana sa ran za a yi wa ɗan wasan tsakiya na Ingila Jordan Henderson tiyata a wuyan hannunsa bayan da ya ji rauni yayin da yake murnar nasarar da ƙasarsa ta samu a zagayen ƴan 16 na gasar cin kofin duniya da Mexico, lamarin da ke jefa shakku kan ko zai iya taka wata rawa a sauran wasannin gasar ta bana.

    Henderson ya faɗo ne daga allon talla da ke kewaye da filin wasan Azteca da ke Mexico City bayan nasarar da Ingila ta samu da ci 3-2, kuma an fitar da shi daga filin wasa a kan gadon ɗaukar marasa lafiya.

    "Jordan [Henderson] ya faɗi kuma ya ji rauni a wuyan hannunsa. Lamarin yana da matuƙar muni," in ji Thomas Tuchel, babban kocin tawagar Ingila, ya shaida wa tashar BBC One bayan nasarar da suka samu.

    "Rauni ne mai tsanani, kuma rashin kasancewar Jordan tare da mu a yanzu bai dace da yanayin wannan dare ba. Likita ya sanar da ni cewa yana asibiti."

    Bayan wasan da aka buga ranar Litinin, wani ma'aikacin tawagar Ingila ya raka Henderson zuwa asibiti a birnin Mexico City, kuma bai koma tare da sauran ƴan wasan zuwa sansaninsu da ke Kansas City ba.

    Ana tunanin cewa ɗan wasan tsakiyar ƙungiyar Brentford ɗin yana da matuƙar sha'awar ci gaba da zama tare da tawagar na tsawon lokacin zaman da za su yi a Amurka.

  16. Queiroz ya sauka daga muƙaminsa na kocin Ghana

    Carlos Queiroz ya sauka daga muƙamin kocin Ghana bayan watanni uku yana jagorantar tawagar bayan sun fice daga gasar cin kofin duniya a zagaye na ƴan 32.

    Kocin mai shekara 73 ya karɓi ragamar horas da tawagar a watan Afrilu kuma ya jagoranci tawagarsa zuwa matsayi na uku a rukunin L kafin Colombia ta doke su da ci 1-0 a zagaye na ƴan 32 na gasar cin kofin duniya.

    Tsohon kocin Manchester United ya je gasar cin kofin duniya sau biyar a jere, bayan ya jagoranci Iran da Portugal da Masar a manyan gasanni.

    Queiroz na ɗaya daga cikin kociyoyin tawagogin ƙasa biyu da suka bar muƙamansu a ranar Lahadi, inda ƙasar Jordan ma ta raba gari da babban kocinta Jamal Sellami bayan tawagar ta zo ta huɗu a Rukunin J.

    A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafukansa na sada zumunta, Queiroz ya bayyana ɗan lokacin da ya yi tare da Ghana a matsayin tafiya mai cike da "alfahari," yana mai yan wasansa sun dawo wa tawagar Black Stars kimarta a fagen wasan ƙwallon ƙafa na duniya.

    Tawagar Black Stars za ta koma fagen wasa a watan Satumba, lokacin da za a fara fafutukar neman gurbin shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka (Afcon) ta shekarar 2027.

  17. Trump ya tabbatar da cewa ya buƙaci FIFA ta sake duba hukuncin dakatar da Balogun.

    Shugaban Amurka Donald Trump ya tabbatar da cewa ya nemi Fifa ta sake duba hukuncin dakatarwar da aka yi wa ɗan wasan gaban Amurka Folarin Balogun na wasa ɗaya a gasar cin kofin duniya.

    Trump ya ce hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya "ta yanke shawarar da ta dace" wajen jingine hukuncin Balogun, inda ya ƙara da cewa da an aiwatar da hukuncin da hakan ya rage karsashin gasar ta bana.

    Balogun, wanda shi ne ɗan wasan tawagar Amurka da ya fi zura ƙwallaye a gasar da ake yi a yanzu, an shirya dakatar da shi ne a fafatawar da ƙasarsa za ta yi da Belgium a wasan zagaye na 16 a Seattle ranar Talata.

    Amma a daren Litinin, Fifa ta jingine hukuncin dakatarwar na wasa ɗaya na tsawon watanni 12, wanda hakan ya ba da damar a zaɓi ɗan wasan gaba mai shekaru 25.

    Da yake magana a Fadar White House ranar Litinin, Trump ya ce ya nemi Fifa ta sake duba hukuncin saboda "bai yi tunanin laifi ba ne".

    Trump ya tabbatar da cewa ya tattauna da shugaban hukumar FIFA Gianni Infantino, amma ya ce abin da kawai ya yi shi ne neman a sake duba lamarin, tare da ƙarin bayanin cewa bai ce wa shugaban na Fifa ɗin ya jingine hukuncin dakatarwar da aka yi wa Balogun ba.

  18. Jordan henderson ya ji rauni a hannunsa yayin murnar nasarar Ingila

    Kocin Ingila Thomas Tuchel ya ce ɗan wasan tsakiya Jordan Henderson ya ji rauni a wuyan hannu yayin da yake murnar nasarar da tawagarb ƙasarsa ta samu a gasar cin kofin duniya a zagayen ƴan 16, inda suka doke Mexico.

    Henderson ya faɗo ne daga allon talla da ke kewaye da filin wasan Azteca da ke Mexico City bayan nasarar da Ingila ta samu da ci 3-2, kuma an fitar da shi daga filin wasa a kan gadon ɗaukar marasa lafiya.

    Ɗan wasan tsakiya na Brentford mai shekaru 36 ya buga minti shida ne kacal a gasar cin kofin duniya inda ya shigo a ƙarshen wasan da Ingila ta doke Panama a rukunin L.

    Wasan Ingila na gaba shi ne na matakin daf da na kusa da na ƙarshe (quarter-final) da Norway a Miami ranar Asabar.

  19. Hukumar ƙwallon ƙafar Belgium ta soki hukuncin FIFA kan Balogun

    Hukumar ƙwallon ƙafa ta Belgium (RBFA) ta bayyana cewa ta yi matuƙar mamakin matakin da FIFA ta ɗauka, na jingine hukuncin jan katin da aka dannawa ɗan wasan Amurka Folarin Balogun, kuma ta ce tana nazarin duka matakan da za ta iya ɗauka a matsayin martani.

    Tsohon shugaban hukumar ƙwallon ƙafar ya shaida wa BBC cewa matakin da Fifa ta ɗauka na jingine hukuncin a matsayin ''rashin adalci ne".

    Folarin Balogun zai samu bugawa Amurka wasan na zagayen ƴan 16 na gasar cin kofin duniya da Belgium bayan da Fifa ta jingine hukunci da aka yi masa na dakatarwar wasa ɗaya bayan shugaban Amurka Donald Trump ya sa baki cikin lamarin.

    An bai wa ɗan wasan gaba mai shekaru 25, wanda shi ne ɗan wasan gaba mafi zura ƙwallaye a gasar da ƙwallaye uku, jan kati kai tsaye saboda ƙetar da ya yi wa ɗan wasan baya na Bosnia-Herzegovina Tarik Muharemovich, yayin da masu masaukin baƙin suka lashe wasansu na ƙarshe na zagayen ƴan 32 da ci 2-0.

    Fifa ta ce za a jingine dakatarwar na tsawon shekara guda.

    Babu wani dalili da ya sa aka ɗauki matakin, sai dai ta ambaci wata doka da ta ba da damar jingine hukunci. Trump ya gode wa Fifa saboda "dakatar da babban rashin adalci" a cikin wani sakonda ya wallafa a shafinsa na dandalin Truth Social.

  20. Glasner ya zama kocin Nottingham Forest na biyar cikin shekara guda.

    Ƙungiyar Nottingham Forest ta naɗa tsohon kociyan Crystal Palace, Oliver Glasner, a matsayin kociyanta na biyar cikin ƙasa da shekara guda.

    Ɗan kasar Austriyan ya iso filin wasa na City Ground ne domin maye gurbin Vitor Pereira, wanda aka kora a ranar Talata - mintuna biyu kacal kafin wa'adin wani sharaɗi na musamman a cikin kwantiraginsa ya ƙare.

    "Oliver mutum ne mai son nasara," in ji mamallakin ƙungiyar Forest, Evangelos Marinakis. "A bayyane yake cewa muna da manufa ɗaya, buri ɗaya, da kuma kishin ganin mun samu nasara ba tare da gajiyawa ba."

    An fara tattaunawa da Glasner, mai shekaru 51 - wanda ya bar Palace a ƙarshen kakar wasan da ta gabata - tun farkon wannan bazarar.

    Nuno Espirito Santo ne ya fara kakar wasan bara a matsayin kocin Forest, yayin da Ange Postecoglou da Sean Dyche da Pereira suka yi aiki tun daga watan Satumba.

    Glasner ya zama kocin Palace ne 2024 kuma ya jagorance su zuwa lashe babbar gasarsu ta farko a kakarsa ta farko - Kofin FA - kafin su lashe gasar Europa Conference League a kakar wasa ta bara.

    Sun lashe Community Shield a watan Agusta, inda suka doke Liverpool da bugun fanareti. A watan janairu ne Glasner ya ce zai bar Palace saboda yana son ya fuskanci wani sabon ƙalubale, duk da cewa an miƙa masa sabon kwantiragi.

    Glasner yana daya daga cikin kociyoyi uku kacal da suka taɓa lashe gasar Europa League da Conference League, bayan ya jagoranci Eintracht Frankfurt zuwa nasara a gasa Europa League a kakar wasa ta 2021-22.