Buƙatun Amurka na son kai ne suka sa aka gaza cimma matsaya - Iran

Asalin hoton, Getty Images
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi, ya ce an gaza cimma matsaya a tattaunawar da suka yi da Amurka a farkon wannan watan da nufin kawo karshen yaƙin ne saboda abin da ya kira '' buƙatun Washington na son rai".
A yayin da ya isa Rasha domin tattaunawa da shugaba Putin, Mista Arachi ya ce tattaunawar zaman lafiyar zagaye na farko a Pakistan ya soma samun nasara, amma kuma daga bisani ya ruguje saboda yadda Amurka ta tunkari tattaunawar.
Kafafen yaɗa labarai na Amurka sun ruwaito cewa Iran ta gabatar da wani sabon ƙuduri ga Washington na yadda za a buɗe mashigar Hormuz da kuma kawo ƙarshen yaƙin, amma kuma ta ɗage batun tattaunawa kan nukiliya zuwa wani lokaci na gaba.




