An zargi gwamnatin Habasha da sake tura sojoji zuwa gabashin Tigray
Ƙungiyar TPLF ta zargi gwamnatin Habasha da sake tura sojoji daga yammacin Tigray zuwa gabashin yankin, matakin da ta ce zai iya ƙara tsananta rikici a yankin.
A wani taron manema labarai da aka yi ranar 30 ga Yuni, shugabar ofishin TPLF, Fetlework Gebrezighiabher, ta ce duk da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Pretoria, gwamnatin na ci gaba da takurawa al’ummar Tigray, har ma ta zarge ta da kashe fararen hula.
Tun da farko, TPLF ta ce gwamnati na kokarin mamaye yankin Tigray da sojoji tare da shirye-shiryen sake fara yaƙi, yayin da gwamnatin Habasha ta maida martani da cewa TPLF ce ke shirin tayar da rikici.
A ɓangaren ƙasa da kasa, Tarayyar Turai da Amurka sun nuna damuwa kan ƙarin fargabar rikici, suna kira da a aiwatar da yarjejeniyar Pretoria gaba daya, sai dai TPLF ta yi watsi da wannan kira.