Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya na 12/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai kai tsaye dangane da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya na ranar Juma'a 12/06/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Usman MINJIBIR da Muslim Muhammad Yusuf

  1. Firaministan Birtaniya ya ce ba zai yi murabus ba

    Firaministan Birtaniya Kier Starmer ya ce ba zai yi murabus daga muƙaminsa ba duk da matsin lambar da ake yi.

    A hirarsa da BBC, Starmer ya ce gwamnatinsa ta ƙara kuɗin da ake ware wa fannin tsaro kuma yana daga cikin abin da ya fi ba muhimmanci.

    Wannan na zuwa ne bayan da Sakataren Tsaron Birtaniya John Healey da mataimakinsa suka yi murabus domin nuna adawa da rashin kasafin kuɗin fannin tsaro mai kyau a ƙasar, da kuma sukar tsarin Starmer.

    Ya shaida wa BBC cewa ya ɗauki matakai masu tsauri domin ganin ya ƙara kasafin kuɗin fannin tsaro.

  2. Gwamnatin Kaduna ta yi wa fursunoni 97 afuwa

    Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya sanar da yi wa fursunoni 97 da ke tsare a gidan gyaran hali na Kaduna afuwa, albarkacin ranar dimokuraɗiyyar Najeriya ta shekarar 2026.

    Sanarwar da gwamnan ya fitar a ranar Juma’a ta ce ya yi musu afuwar ne sakamakon ikon da kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 ya ba shi.

    Gwamnan ya ce: “Mun yi imanin cewa kowane mutum ya cancanci wata dama ta biyu da kuma damar sake gina rayuwarsa."

    "Ina kira ga wadanda suka ci gajiyar wannan afuwa da su yi amfani da damar, su rungumi kyawawan ɗabi’u tare da koyon sana’o’i da za su ba su damar bayar da gudunmawa mai amfani ga al’umma,” in ji shi.

    Uba Sani ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa shirye-shiryen gyaran hali da sake shigar da waɗanda aka yi wa afuwar cikin al’umma domin su amfani iyalansu da yankunansu.

  3. An kashe ƴan ta'adda "sama da 13,000" a Najeriya cikin shekara ɗaya - Tinubu

    Sojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda "sama da 13,000" a cikin shekarar da ta gabata, in ji shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu

    Kalamansa na zuwa ne a daidai lokacin da ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai da masu aikata laifuka ke ci gaba da kai hare-hare da garkuwa da mutane a ƙasar.

    A wani jawabi da ya yi ta kafar talabijin na ƙasar a ranar Juma’a, domin murnar cikar ranar dimokraɗiyyar Najeriya, shugaba Tinubu ya ce adadin waɗanda suka mutu a yaƙin da Najeriya ke yi da ƴan bindiga ya ragu da kashi 81 cikin 100 tun bayan da ya hau mulki a shekarar 2023.

    Tinubu ya ce a daidai lokacin da ƙasar ke murnar cikarta shekaru 27 da mulkin dimokraɗiyya ba tare da samun tangarɗa ba, abubuwa biyu marasa daɗi sun faru da suka haɗa satar yara ƴan makaranta a Oyo da Borno.

    Tinubu ya ƙara da cewa: "Mayaƙa 124,000 sun ajiye makamansu tun daga shekarar 2023 ta hanyar Operation Safe Corridor," shirin da ke sauya tunanin tubabbun ƴan bindiga waɗanda suka ajiye makamansu bisa raɗin kansu.

    To sai dai kuma duk da nasarar da ya ce ya yi a jawabin nasa, ƙasar na cikin mawuyacin hali na taɓarɓarewar tsaro da ya sa ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai masu alaƙa da ISIL (ISIS) da al-Qaeda ke sace ƴan ƙasar domin neman kuɗin fansa.

  4. Ba zan taɓa bari Iran ta mallaki makamin nukiliya ba - Netanyahu

    Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce ba zai taɓa bari Iran ta mallaki makamin nukiliya ba.

    Kamar yadda ya wallafa a shafinsa na X, Netanyahu ya ce: "In dai ni ne Firamnistan Isra'ila, Iran ba za ta mallaki makamin nukiliya ba."

    Ya ƙara da cewa: "Wannan ita ce matsayar da aka cimma tsakani na da Trump kan maganar."

    Ya yi iƙirarin cewa ya kwashe shekaru 30 yana yaƙar yunƙurin Iran na mallakar makamin nukiliya.

    Netanyahu ya ce ba don ƙoƙarin da ya yi ba, da yanzu Iran ta mallaki makamin nukiliya kuma ta ruguza Isra'ila tun da ɗaɗewa.

    "Iran na son ganin ta ruguza ƙasar Yahudawa, kuma na sadaukar da rayuwata wajen ganin wannan burin bai cika ba," in ji shi.

    Wannan ne karon farko da Netanyahu ya yi magana bayan da Trump ya ce an cimma matsaya da Iran, kuma ya fasa kai mata hare-haren da ya yi niyyar ƙaddamarwa a daren Alhamis.

  5. An cimma yarjejeniya tsakanin Iran da Amurka, in ji Firaministan Pakistan

    Ƙasar Pakistan mai shiga tsakanin Amurka da Iran a tattaunawar sulhu kan yaƙin da ƙasashen ke yi ta ce an cimma matsaya.

    Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif ne ya sanar da cewa an cimma matsaya ta ƙarshe tsakanin ƙasashen biyu, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na X.

    "A ƙoƙarin da Pakistan ke yi na shiga tsakani, muna sane da jita-jitar da ake yaɗawa domin lalata tattaunawar samar da zaman lafiyar da ake yi. Amma dai yanzu muna iya tabbatar da cewa an cimma matsaya ta ƙashe, kuma a yanzu haka Pakistan na aiki da duka ɓangarorin biyu domin kammala mataki na gaba," a saƙon da Mr. Sharif ya wallafa a shafinsa na X.

    "Saura ƙiris a samu zaman lafiya," in ji shi.

    Shi ma ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya wallafa cewa an kusa cimma matsaya da fahimtar da juna tsakaninsu da Amurka "kuma saura ƙiris".

    Shugaban Amurka Donald Trump ma ya sake wallaga saƙon na Araqchi a shafinsa na X.

  6. An gudanar da zanga-zangar rashin tsaro a ranar dimokraɗiyyar Najeriya

    Wasu matasa sun fantsama kan titunan birnin tarayyar Najeriya da wasu jihohi domin nuna ɓacin ransu kan ƙaruwar matsalar tsaro a ƙasar.

    Zanga-zangar na zuwa a daidai lokacin da ƙasar ke bikin tunawa da ranar dimokraɗiyyar ƙasar da aka shafe shekaru 27 ba tare da yankewa ba.

    Matasan sun buƙaci shugaban ƙasar Bola Tinubu ya yi gaggawar ɗaukar matakin da ya dace domin magance matsalar tsaro a sassan ƙasar.

    Ɗan gwagwarmaya Omoyele Sowore ya jagoranci zanga-zangar rashin tsaron a birnin tarayya Abuja, inda ya yi kira ga shugaba Tinubu ya yi gaggawar ceto ɗaliban da aka sace a jihar Oyo.

    Sowore ya kuma yi ƙorafi kan matsin rayuwa da ake ciki a Najeriya da rashin samun ci gaba da kuma garkuwa da mutane.

    Ya ce ƙasar ba ta samu wani ci gaban da ya kamata ba duk da an shafe shekaru 33 da komawa tsarin ɗimokradiyya, inda ya yi kira ga Tinubu ya yi murabus idan ba zai iya kare rayukan ƴan ƙasar ba.

    A jihar Osun ma matasa sun fantsama kan titunan birnin jihar domin nuna damuwarsa kan halin da ƙasar ke ciki.

    Ƙungiyoyin sa kai sun shiga zanga-zangar, inda suka soki salon mulkin Bola Tinubu kan matsalar tsaro da tsadar rayuwa a ƙasar.

    Wani matashi Saka Lawal ya shaida wa BBC cewa bai taɓa ganin mulkin da ake shan wahala irin na wannan lokacin ba.

    "Muna buƙatar shugaba Bola Tinubu ya yi gaggawar magance matsalolin da Najeriya ke ciki kafin abin ya wuce gona da iri" in ji shi.

  7. Kwamandojin ISWAP biyu sun miƙa wuya ga sojin Najeriya - Su wane ne su?

    Wasu manyan kwandojin ƙungiyar ISWAP su biyu sun miƙa wuya ga rundunar sojin Najeriya.

    Rundunar sojin ƙasa ta Najeriyar ce ta sanar da cewa mutanen masu suna Ismail Mohammed da Abu Umar da suka miƙa wuya yanzu suna tsare a hannunta kuma suna ci gaba da bayar da bayanai masu muhimmanci, kamar yadda ta sanar.

    "Rundunar Operation HADIN KAI sun samu wata gagarumar nasara a yaƙi da take yi da ta'addanci bayan da wasu manyan kwamandojin ƙungiyar ISWAP biyu suka miƙa wuya ga dakarunmu a ranar 8 ga watan Yuni 2026," in ji muƙaddashin jami'in yaɗa labarai na rundunar Haruna Sani.

    Ku karanta cikakkun bayani kan kwamandojin a nan.

  8. Jiragen ruwa 50 na jiran izinin wucewa ta Hormuz

    Hukumar Rediyo da Talabijin ta Iran ta ce “kimanin jiragen ruwa 50” ne ke jiran a mashigar Hormuz domin rundunar sojin ruwa ta Juyin Juya Hali ta ba su izinin wucewa.

    Wannan na zuwa ne yayin da Hukumar Kula da Hanyoyin Ruwa ta Tekun Farsi ta sanar a ranar Alhamis cewa an rufe mashigar ga jiragen kasuwanci da tankokin mai har sai an sake bayar da wata sanarwa, sakamakon tashin hankalin da ke tsakaninta da Amurka.

    Hukumar ta kuma bayyana cewa jiragen da suka samu “izinin wucewa” su ci gaba da jiran ƙarin umarni.

    “Yankin yammacin mashigar Hormuz, mashigar kanta, da kuma Tekun Farsi na karkashin cikakken ikon rundunar sojin ruwa ta IRGC, yayin da gabashin mashigar Hormuz da arewacin Tekun Indiya ke karkashin ikon rundunar sojin ruwa ta sojin ƙasa. Babu wani jirgin ruwa da zai iya shiga wannan mashiga ba tare da izininmu ba," in ji Habibollah Sayyari, Babban Hafsan Sojin Iran kuma mataimakin mai kula da rundunar.

  9. Trump na shirin mayar da ƴan ciranin Iran zuwa Afirka ta tsakiya

    Gwamnatin Trump na shirin mayar da wasu ‘yan ƙasar Iran da wasu bakin haure zuwa Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, wata ƙasa da ta kwashe shekaru tana fama da rashin kwanciyar hankali da talauci mai yawa, kamar yadda lauoyoyi biyu da wani jami’i da suka san batun suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

    A cewar Emily Trussell, lauya mai kare wasu daga cikin waɗannan ƴan ciranin ya ce cikin Iraniyawan da ke fuskantar kora akwai mata biyu da za su iya fuskantar azabtarwa da cin zarafi idan aka mayar da su Iran.

    A wata hira da Reuters, ta ƙara da cewa a wata hira da Reuters, ɗaya daga cikin matan ta koma addinin Kiristanci, yayin da ɗayar kuma ta kasance mai fafutukar dimokuraɗiyya.

    Reuters ya ruwaito cewa Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka da ofishin shugaban Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya — ƙasar da kwanan nan ta cimma yarjejeniya don karɓar bakin hauren da Amurka ke kora daga wasu ƙasashe — ba su mayar da martani ba game da buƙatun tabbatarwa ko ƙarin bayani kan rahoton.

    Wani jami’i da ya san batun ya shaidawa Reuters cewa jirgi na farko zuwa Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya karkashin yarjejeniyar ana sa ran zai ɗauki kimanin mutane 20, ciki har da wasu ‘yan ƙasar Siriya da Afghanistan, baya ga Iraniyawa.

    A cewar wasu lauoyoyi biyu da suka san batun, jirgin na iya tashi a ranar Alhamis.

  10. Hezbollah ta ce ta kai hare-hare 24 kan sojojin Isra'ila

    Kungiyar Hezbollah ta Lebanon ta ce ta kai jerin hare-hare da jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami da rokoki kan sojojin Isra’ila da a kudancin Lebanon da yankin Bekaa Valley.

    A wata sanarwa da ta yi bayani kan ayyukan kungiyar daga ranar Laraba zuwa Alhamis, Hezbollah ta ce ta kai hari kan taron sojojin Isra’ila da kuma motocin yaƙi masu sulke.

    Kungiyar ta yi ikirarin cewa wadannan hare-hare sun mayar da hankali musamman kan yankin Al-Rajman, kusa da Tayyir Harfa, inda aka kai hare-hare sau hudu a lokuta daban-daban.

    Sanarwar ta kara da cewa an kuma kai hare-hare kan wuraren taruwar sojojin Isra’ila da motocinsu a garuruwan Lebanon da suka hada biranen Naqoura da Al-Quwazeh da Rashaf da Al-Qantara da kuma Zutar Al-Sharqiya da Yawmar Al-Shaqif.

  11. Misra ta yi kira ga Iran da Amurka da su cimma yarjejeniya

    Misira ta yi kira ga Iran da Amurka da su yi amfani da “damar da ake da ita a yanzu” don cimma yarjejeniya da za ta kawo ƙarshen yaƙin da suke yi.

    Ma’aikatar Harkokin Wajen Misira ta bayyana wannan kira a cikin wata sanarwa bayan Shugaban Amurka Donald Trump ya janye barazanar ci gaba da kai hare-hare kan Iran.

    Masu sharhi kan al'amuran da suke da masaniya kan halin da ake ciki sun zayyana wasu abu guda huɗu da suka ce su ne ke tarnaƙi ga cimma sulhu tsakanin Iran da Amurka.

  12. Tawagar ƙwallon ƙafar DRC ta isa Amurka domin buga gasar Kofin Duniya

    A karshe, tawagar 'yan wasan ƙwallon ƙafar Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ta isa Amurka domin halartar gasar cin kofin duniya, bayan ta shafe kwanaki 21 a keɓe saboda ɓarkewar cutar Ebola a ƙasar da ke tsakiyar Afirka.

    Tawagar ta sauka a birnin Houston a jiya ranar Alhamis, bayan ta shafe lokaci tana shirye-shiryen gasar a ƙasar Belgium.

    Za dai ta buga wasanta na farko da ƙasar Portugal a ranar Laraba.

    Kocin tawagar, Sebastien Desabre, ya ce yana fatan 'yan wasansa za su taka rawar gani domin farantawa ƙasarsu da ke fuskantar ƙalub.

  13. Dimokraɗiyya ba tare da tsaro ba tamkar ba ta zauna ba - Tinubu

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya nemi ƴan najeriya da su ƙaunaci Najeriya duk da irin matsalolin da ƙasar ke fama da su musamman matsalar tsaro.

    A jawabinsa na ranar dimokraɗiyya, Tinubu ya ce a daidai lokacin da ƙasar ke murnar cikarta shekaru 27 da mulkin dimokraɗiyya ba tare da samun tangarɗa ba, abubuwa biyu marasa daɗi sun faru da suka haɗa satar yara ƴan makaranta a Oyo da Borno.

    Tinubu ya ce dimokraɗiyya ba tare da tsaro ba to tamkar ba ta yi ƙwari ba, inda ya ƙara da cewa hakan ne "ya sa gwamnatin ta ayyana ta-ɓaci kan matsalar tsaron sannan kuma ta amince ɗaukar ƴan sanda fiye da 50,000 da kuma dubban sojoji.

    Daga ƙarshe Tinubu ya jinjina wa marigayi Alhaji Mashood Abiola wanda ake bikin ranar saboda shi wanda ya ce ya yi siyasa kuma ya samu goyon bayan jama'a daga ɓangarorin addini da na al'adu daban-daban.

  14. An yankewa Yoon Suk Yeol na Koriya ta Kudu hukuncin shekaru 30 a yari

    An yankewa tsohon shugaban ƙasar Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol, hukuncin daurin shekaru talatin a gidan yari bisa tuhume tuhumen bayar da umarnin aika jirage marasa matuƙa zuwa Koriya ta Arewa.

    Wakilin BBC ya ce zaman dar dar tsakanin kasashen biyu ya karu ne a 2024, bayan da wani jirgi marar matuki ya watso da wasu takardu cikin babban birnin Koriya ta Arewa.

    Kotun ta ce hakan yunkuri ne na tunzura Pyongyang ta mayar da martani ta hanyar kai hari domin tabbatar da cewa ta karya dokar kawo karshen mulkin soji da aka ayyana.

    Mista Yoon ya fuskanci shari’o’i da dama tun bayan da aka tsige shi daga kan mukaminsa saboda yunƙurinsa na kafa mulkin soji a watan Disambar 2024.

    A watan Fabrairu, an same shi da laifin tayar da ƙayar baya, inda aka yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

  15. Har yanzu ba mu fitar da matsaya ba kan yarjejeniya da Amurka - Iran

    Iran ta jaddada cewa har yanzu ba ta kai ga yanke hukunci na ƙarshe ba akan yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙin da Amurka ke yi da ita, duk da cewa Shugaba Trump ya sake nanata cewa akwai yiwuwar nan bada jimawa ba za a sanya hannu akan yarjejeniyar.

    Da yake jawabi ga dandazon magoya bayansa ta bidiyo a daren ranar Alhamis, Mista Trump ya shaida wa taron cewa: “A yau mun kawo ƙarshen yaƙin da muke da Iran.”

    Da dama daga irin waɗannan iƙirarin a baya na cewa yaƙin na gab da ƙarewa ba su tabbata ba, sai dai sabbin kalaman shugaban sun sake ƙarfafa kasuwannin hannayen jari, tare da jawo farashin mai ya sauka.

    Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta ce a halin yanzu tana nazarin ƙunshin yarjejeniyar da aka gabatar mata, amma Tehran ba za ta yi sassauci kan mahimman sharuɗɗanta ba.

  16. Abu huɗu da za su iya hana ɗorewar tsagaita wuta tsakanin Iran da Amurka

    Yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran, wadda aka cimma a farko-farkon watan Afrilu, yanzu za a iya cewa tana kan gargarar watsewa bayan jerin hare-haren da suka faru a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Shugaban Amurka Donald Trump da wani babban jami'in Iran sun yi musayar barazana a farkon watan Afrilu, sannan kuma sun sha alwashin ci gaba da ɗaukar matakai kan juna bayan musayar hare-hare.

    A ranar Laraba, Amurka ta ce ta kai hari kan na'urorin tattara bayanai na Iran bayan Iran ta kakkaɓo ɗaya daga cikin helikwaftocinta na soji a yankin Gulf.

    Dakarun juyin juya hali na Iran na mayar da martani ta hanyar kai hari kan sansanonin sojin Amurka a Bahrain da Jordan, sai dai Kuwait ta ce ta tare wasu hare-haren.

    Sake farfaɗowar yaƙin ya zo ne kwanaki bayan Iran ta kai hari da makamai mai linzami kan Isra'ila a ranar Lahadi, lamarin da ya sanya Isra'ila ta mayar da martani ta hanyar kai hare-hare a yammaci da tsakiyar Iran - wanda shi ne karon farko da aka yi musayar wuta kai-tsaye tsakanin angarorin biyu tun bayan yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma.

  17. Me ya faru a ranar 12 ga Yunin 1993?

    Zaɓen shugaban ƙasa na ranar 12 ga watan Yunin 1993, shi ne na farko a Najeriya bayan juyin mulki na 1983.

    Zaɓen ya ƙunshi jam'iyyu biyu; Social Democratic Party (SDP) da National Republican Convention (NRC) sakamakon Najeriya na amfani ne da tsarin jam'iyyun siyasa biyu.

    Moshood Kashimawo Abiola (MKO) ne ɗan takarar shugaban ƙasa na SPD, yayin da Bashir Tofa ya yi wa NRC takara.

    Masu sa ido na ciki da wajen Najeriya na ganin zaɓen 12 ga Yuni a matsayin mafi inganci, amma sai aka yi watsi da shi.

    Abubuwan da suka faru da kuma tasirinsu sun ci gaba da zama a zukatan 'yan Najeriya.

    Yana cikin abubuwan da suka mamaye tarihin Najeriya, sannan ranar ta 12 ga Yuni za ta ci gaba da zama ta musamman.

    Domin karanta cikakken labarin ku latsa nan

  18. Wane ne Mahdi, yaushe zai bayyana kuma a ina?

    Kusan ilahirin al'ummar Musulmin duniya sun yi imani cewa a ƙarshen zamani za a yi wani mutum bawan Allah mai suna Mahdi wanda zai yaƙi zalunci sannan ya tabbatar da adalci.

    Sai dai kuma fahimtar wane ne Mahdi da kuma haihuwarsa sun kasance wasu abubuwa masu taƙaddama a tsakanin mazhabobi da ɗariƙu daban-daban.

    Wannan ya sa a tarihi aka samu wasu mutane a baya da suka ayyana kansu a matsayin Mahdi to amma idan tafiya ta yi tafiya sai jama'a su fahimci al'amarin ba haka yake ba - duk da cewa dai rasuwar mai iƙrarin kasancewa Mahdi ba ta sauya wa wasu ra'ayi.

    Wataƙila hakan ne ma ya sa wasu da suka haɗa da malami da waɗanda suka yi imani da zahiri ke da fahimtar cewa babu wani Mahdi da zai zo a ƙarshen zamani.

    Domin sanin haƙiƙanin yadda al'amarin yake, BBC ta tattauna da malamai daga fahimta daban-daban ta addinin Musulunci domin sanin abin da kowane ɓangare ya yi imani da shi dangane da Mahdi.

    Ku latsa nan domin karanta cikakken labarin

  19. Buɗewa

    Masu bibiyarmu barka da safiyar ranar Juma'a. Muna yi wa abokan hulɗarmu na Najeriya murnar cikas ƙasar shekaru 27 na mulkin dimokraɗiyya ba tare da samun tangarɗa ba. Da fatan za a sha hutun ranar ta dimokraɗiyya lafiya.

    To sai dai ka da a manta wajen ci gaba da kasance wa da shafin kai tsaye na BBC Hausa wanda ke kawo muku sahihan labarai kuma da ɗumi-ɗuminsu dangane da irin wainar da ake toyawa a Najeriya da sauran sassan duniya. Mun gode!