Ƴanbindiga sun sace malamai shida bayan halartar addu'ar neman nasarar Tinubu

Asalin hoton, Getty Images
Ƴansanda a Najeriya sun ce wasu ƴanbindiga sun sace limamai shida a jihar Zamfara da ke arewacin ƙasar.
Lamarin ya faru ne a ranar Asabar, lokacin da limaman suka halarci wani taron addu'a na neman nasarar Shugaba Bola Tinubu, wanda ke neman wa'adi na biyu a babban zaɓen da za a gudanar a watan Janairu.
Sace mutane domin neman kuɗin fansa ya zama babbar hanyar samun kuɗaɗen shiga ga ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai da dama a Najeriya, ciki har da masu iƙirarin jihadi da kuma ƙungiyoyin ƴanbindiga waɗanda ba su da wata manufa ta aƙida, waɗanda ke neman kuɗin fansa kafin su saki mutanen da suka yi garkuwa da su.
Rashin tsaro da kuma halin da tattalin arzikin ƙasar ke ciki na daga cikin manyan batutuwan da suka mamaye yaƙin neman zaɓen da ake gudanarwa a yanzu.
Sai dai a wata sanarwa da rundunar sojin ta Fansar Yamma ta fitar, ta ce bincikensu ya tabbatar da cewa ba a gidan Abdulaziz Yari aka sace malaman ba.
"Mun dai samu labarin cewa an sace wasu mutane matafiya da suka taso daga yankin dajin Sububu zuwa Talata Mafara, kuma jami'anmu da haɗin gwiwar sauran jami'an tsaro suna ƙoƙarin ceto," in ji sanarwar.


















