KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 26/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Lahadi 26 ga watan Yulin 2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal

Rahoto kai-tsaye

Aisha Babangida da Isiyaku Muhammed

  1. Ƴansanda na neman matashin da ya kutsa taron masu neman jinsi a Jamus

    Berlin

    Asalin hoton, Getty Images

    'Yan sanda a birnin Berlin na Jamus sun shafe dare suna neman direban wata mota da ta kutsa cikin taron mutane a ɗaya daga cikin manyan tarukan masu neman jinsi daya a Turai, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mace daya da jikkata mutum 16.

    Wakilin BBC ya ce 'yansanda na amafani da jirgin sama mai saukar ungulu da fitilu masu haske a neman wanda ake zargin a cikin duhun wannan waje na tsakiyar Berlin.

    Hukumomi sun ce babban wanda ake zargin matashi ne mai shekara 21 mai suna Abdul B, kuma yana da alaka da masu tsattsauran ra'ayi na ikirarin jihadi.

    'Yan sanda sun kuma ce an caka wa wasu daga cikin waɗanda abin ya shafa wuƙa bayan aƙalla mutum ɗaya daga cikin maharan ya fito daga cikin motar kafin ya tsere daga wurin.

    Dubban mutane ne suka halarci taron na shekara-shekara na masu rajin kare haƙƙin masu neman jinsi daya, a babban birnin na Jamus, gangamin da ake wa lakabi da Christopher Street Day.

  2. Trump zai dakatar da yunƙurin faɗaɗa hare-hare a Iran

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni da dama daga Amurka sun ce Shugaba Donald Trump ya yanke shawara, a halin yanzu aƙalla, kada ya ƙara faɗaɗa hare-haren sojin Amurka kan Iran.

    Rahotannin sun ce Trump ya ɗauki matakin ne shekaran jiya Juma'a, bayan da wasu jami'ai suka nuna damuwa game da raguwar makamai masu linzami na kariya na Patriot, masu tsada sosai, da kuma yiwuwar matakin ya haifar da saɓani tsakaninsa da ƙawayen Amurka na ƙasashen Larabawa da ke yankin Tekun Fasha.

    Har yanzu babu wata sanarwa a hukumance kan lamarin, sai dai Fadar White House ta ce Trump koyaushe ya fi son a warware matsaloli ta hanyar diflomasiyya.

    Daren Juma'a ne karo na farko cikin kusan mako biyu da ba a kai hare-haren sama na Amurka kan Iran ba. Haka kuma ba a kai irin waɗannan hare-hare ba a daren Asabar.

  3. Farawa

    Barka da zuwa shafin BBC Hausa na kai-tsaye wanda ke kawo muku labaran duk muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da saurarn sassan duniya a wannan rana ta Lahadi.

    Aisha Babangida ke sake fatan kasancewa da ku a wannan lokaci.

    Za kuma ku iya yin tsokaci a shafukanmun na sada zumunta: facebook, X, instagram, YouTube sai kuma zaurenmu na WhatssApp.