Mayaƙan Houthi sun ce sun kai wa jiragen ruwan Saudiyya hari a Tekun Maliya
Ƙungiyar Houthi ta Yemen ta ce ta kai hari kan wani jirgin ruwan sojan Saudiyya da wasu jiragen ruwa huɗu da ke masa rakiya a Tekun Maliya.
Kakakin rundunar sojan Houthi, Yahya Saree, ya ce an kai harin ne da makamai masu linzami.
Ƙungiyar ta ce daya daga cikin jiragen sojan na Saudiyya na dakon kaya ne, yayin da sauran huɗun da ke masa rakiya jiragen sintiri ne, kuma an kai harin ne kusa da gabar birnin Mokha na Yemen.
Sai dai Saudiyya ba ta fitar da martani kan ikirarin Houthi ba.