KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a ranar Talata 08/09/2026

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Adeyemi Adeniyi
  • Abdourahamane Tchiani
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir

Rahoto kai-tsaye

Daga Muslim Muhammad Yusuf

  1. Muna da ƙarfin ikon kai wa jiragen ruwan Amurka hari - Iran

    Iran

    Asalin hoton, iRNA

    Muƙaddashin ministan tsaron Iran Majiɗ Ibn-e-Reza, ya ce dakarun sojin ƙasar suna da ƙarfin ikon kai hari kan jiragen ruwan yaƙin Amurka.

    A cikin ƴan kwanakin da suka gabata, jami'an Iran sun yi iƙirarin cewa sun kai hari kan jiragen ruwan yaƙin Amurka guda biyu a Tekun Fasha, ta hanyar amfani da makamai masu linzami da ake amfani da su wajen kai hari kan jiragen ruwa.

    Sakataren majalisar ƙoli ta tsaron ƙasa ta Iran, Mohsen Rezaei, ya ce cikin sa'o'i 48 da suka gabata, dakarun sojin Iran sun samu damar gwada makamin da aka ƙera a ƙasar.

    Ya ce: “A karon farko, mun gwada wani makami mai linzami na Iran da aka ƙera domin kai hari kan jirgin yaƙi, a kan wani jirgin ruwan Amurka. Wannan makami ya jefa Amurkawa cikin wani hali na tashin hankali, kuma suka gudu.”

    Rundunar Tsakiyar Sojin Amurka, CENTCOM, ba ta mayar da martani kai tsaye kan iƙirarin Iran ba.

    Sai dai jiya, a wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X, ta yi alamar cewa ta na magana ne kan harin da aka ce an kai wa jiragen ruwanta guda biyu.

    Ta ce: “Idan kuka harbi jiragen ruwanmu guda biyu, za mu kakaba muku wani mummunan takunkumin tattalin arziki, tare da lalata jiragen ruwanku guda uku.”

    CENTCOM ta ƙara da cewa ba za ta yi ƙasa a gwiwa wajen kare sojojin Amurka ba, kuma idan ya zama dole, za ta lalata jiragen ruwan dakon mai na Iran.

  2. Me zai faru idan ɗalibi ya kasa biyan bashin NELFUND?

    NELFUND

    Asalin hoton, NELFUND

    A ƙarshen makon da ya gabata ne wata sabuwar dambarwa ta ɓarke a Najeriya game da biyan bashin karatu da gwamnatin ƙasar ta ɓullo da shi na NELFUND.

    Mahawarar ta ɓarke ne bayan da aka fitar da hoton wata jarida ɗauke da wani labari da ke nuna shugaba Bola Tinubu ya amince da hukuncin ɗaurin rai-da-rai kan ɗaliban da suka gaza biyan bashin da suka karɓa daga asusun ba da Lamunin karatu na Najeriya (NELFUND).

    Wannan labarin dai ya tayar da ƙura tsakanin ɗaliban ƙasar musamman waɗanda suka amfana daga shirin lamunin, lamarin da ya sanya daya

  3. Barka da Safiya!!!

    Masa

    Asalin hoton, Getty Images

    Masu bibiyarmu a wannan shafi na kai tsaye daga BBC Hausa muna muku barka da safiyar Talata.

    Muslim Muhammad Yusuf tare da sauran abokan aiki ne za mu kasance da ku.

    Za ku iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin kallon wasu hotuna da bidiyon hirarraki da muke wallafawa tare da yin tsokaci a kai.