'Mayaƙan Houthi da na al-Shabab na yunƙurin ƙwace Mashigar Bab al-Mandab'

Asalin hoton, Mohammed Hamoud/Getty Images
Jaridar The Telegraph ta Birtaniya ta wallafa wani rahoto mai taken: "Mayaƙan Houthi na shirin buɗe sabon babi a yaƙin Iran, bayan yunƙurin rufe wata muhimmiyar mashigar ruwa ta biyu."
Jaridar ta ce mayaƙan Houthi, waɗanda a yanzu ake kallonsu a matsayin mafiya ƙarfi cikin ƙungiyoyi masu alaƙa da Iran a yankin, suna shirye-shiryen rufe mashigar Bab al-Mandab domin amfanin Iran, da nufin ƙara matsin lamba kan shugaban Amurka Donald Trump, lamarin da zai iya ƙara jefa tattalin arzikin duniya cikin matsala.
Rahoton ya ce akwai haɗin gwiwa tsakanin mayaƙan na Houthi da ƙungiyar al-Shabaab da ke Somalia, wanda manufarsu ita ce mallake ɓangarori biyu na mashigar Bab al-Mandab tare da rufe ta idan Iran ta yanke shawarar yin hakan.
Rahoton ya ambato wata majiya da ta ce mayaƙan Houthi na miƙa fasahar ƙera da amfani da jiragen sama marasa matuƙa (drones) na Iran ga ƙungiyar al-Shabaab bisa umarnin Tehran.
Manufar hakan, in ji rahoton, ita ce haifar da yanayi a Bab al-Mandab mai kama da wanda ake gani a mashigar Hormuz.
Jaridar ta ce kimanin kashi 10 zuwa 12 cikin 100 na cinikayyar duniya na bi ta mashigar Bab al-Mandab, wadda ke haɗuwa da Mashigar Suez.
Telegraph ta yi gargaɗin cewa idan aka rufe mashigar, jiragen ruwa za su tilasta bin wata hanya ta daban wadda za ta ƙara musu makonni suna zagayawa ta kudancin Afirka, lamarin da zai ƙara kuɗaɗen sufuri.


