Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 3/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin, 3 ga watan Agustan 2026

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Wannan ce damar Iran ta ƙarshe -Trump

    ,

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Trump na Amurka ya dage kan cewa za a ci gaba da tattaunawa da Ira domin neman mafita ga rikicin da ke faruwa tsakanin kasashen biyu.

    Da yake tattaunawa da manema labarai a afishinsa da ke Fadar White House a yau, Shugaban Amurkan Donald Trump ya ce wannan ce ‘damar Iran ta karshe domin sanya hannu kan yarjejeniyar’.

    Ya kuma jaddada za a yi tattaunawar ne saboda Iran ta nemi hakan. Duk kuwa da cewa ta fito karara ta musanta cewa hakan bukatarta ce.

    Hakan na zuwa ne lokacin da Trump ya zargi ‘yan siyasar Iran da ‘munafirci’ a shafinsa na Truth Social.

    Ya rubuta cewa “Su ne suka nemi a tattauna, ko kuma kamar yadda wasu suke cewa sun roka ne; a tattauna da kuma wasu taruka nan ba da jimawa ba’’.

  2. Jiragen kasuwanci sun fara wucewa ta mashigar Hormuz – Kepler

    Alƙaluma daga kamfanin Kepler da ke bibiyar lamuran jiragen ruwan kasuwanci sun nuna cewa wasu jiragen kasuwanci ƙalilan sun fara wucewa ta mashigar Hormuz.

    A cewar alƙaluman kamfanin jiragen 51 sun fice ta mashigar tsakanin ranar 30 ga watan Yuli zuwa 2 ga watan Agusta.

    Alƙaluman sun kai kashi 28 idan aka kwatanta da kwanaki huɗu da suka wuce, lokacin da aka rawaito yawan jiragen sun kai kashi 71.

    A cewar rahoton tun 30 ga watan Yuli kimanin jirage 30 ne suka wuce suka nufi Iran.

  3. Ministan harkokin wajen Iran ya sauka a Najaf da ke Iraƙi

    .

    Asalin hoton, @s_a_araghchi

    Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Aracqchi ya isa Najaf da ke Iraƙi.

    Dalilin tafiyar dai shi ne halartar bikin Arbaeen, kuma an bayyana hakan a hukumance.

    Mista Araqchi ya wallafa wani hotonsa lokacin da ya sauka a Najaf a manhajar Telegram.

    Tafiyar Araqchi na zuwa ne daidai lokacin da Donald Trump yake cewa tattaunawa tsakaninsu da Iran za ta fara ne a yau Litinin.

    Esmail Baghaei, kakakin ma'aikatar wajen Iran da yake mayar da martani kan batun tattaunawar da Trump ya yi magana , ya ce shi bai san komai ba kan sanarwar da Trump ɗin ya fitar.

  4. An sace fetur ɗin Birtaniya na £200,000 tun bayan fara yaƙin Iran

    A

    Masu hasashe daga sashen da ke kula ɓangaren man Birtaniya sun gano cewa direbobi suna sace mai na kimanin fan dubu 200 daga man ƙasar a kullum tun lokacin da aka fara faɗan Iran kuma farashin ya tashi.

    Alƙaluma daga Forecourt Eye, wani shafin intanet da yake taimaka wa tashoshin gas kare asarar da suke yi da kuma karɓar bayanansu, ya nuna cewa man da ake ɗiba ba a biya ya ƙaru da kashi 20 a cikin wata biyar tun lokacin da yaƙin Amurka da Iran ya fara a watan Fabirairu 28.

    Yaƙin da aka fara a Gabas ta Tsakiya ya janyo koma bayan samar da mai a yankin, abin da ya janyo tashin farashin man har ma da Burtaniya.

  5. Iran ta musanta ikirarin Trump kan sabuwar tattaunawa da Amurka

    Esmail Baghaei

    Asalin hoton, Getty Images

    Mai magana da yawon ma'aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya jefa shakku kan ikirarin Shugaban Amurka, Donald Trump, cewa ƙasashen biyu za su fara wata sabuwar tattaunawa daga yau.

    Baghaei ya ce a halin yanzu babu wata tattaunawa da ke gudana tsakanin Tehran da Washington, yana mai ƙara da cewa gwamnatin Iran ba ta shirya karɓar wata tawagar Amurka ko aika jami'anta domin ganawa da takwarorinsu cikin ƴan kwanaki masu zuwa ba.

    Ya ce maimakon haka, Iran ta fi mayar da hankali kan tattaunawar da take yi da Oman dangane da yadda za a tafiyar da zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigar Tekun Hormuz.

    Wakiliyar BBC ta ruwaito Baghaei na cewa Iran da Oman na tattaunawa ne kan samar da wata sabuwar hanyar zirga-zirgar jiragen ruwa mai hanyar shiga da ta fita.

    Sai dai ya jaddada cewa amincewa da irin wannan tsari kaɗai ba yana nufin za a buɗe Mashigar Tekun Hormuz ba.

    Donald Trump dai bai bayyana ko su waye jami'an da ya ce suna tattaunawa da Iran ba, haka kuma bai fayyace inda ake gudanar da tattaunawar ba.

    A gefe guda kuma, farashin gangar ɗanyen mai ya ragu lokacin da aka buɗe kasuwannin duniya a yau.

  6. An gana da tsohuwar shugabar Myanmar da ke tsare a karon farko daga kurkuku

    Aung San Suu Kyi

    Asalin hoton, Getty Images

    Dangin tsohuwar shugabar Myanmar da ke tsare a hannun gwamnatin soji, Aung San Suu Kyi, sun yi maraba da damar da aka ba ta na ganawa da wasu jami'an ƙungiyar agaji ta Red Cross.

    Ganawar ita ce ta farko da aka tabbatar Suu Kyi ta yi da wasu mutane daga wajen gidan yari cikin fiye da shekara biyu da rabi.

    Ɗanta, Kim Aris, ya ce an ba shi tabbacin cewa hotunan da gwamnatin sojin Myanmar ta fitar, waɗanda ke nuna mahaifiyarsa cikin ƙoshin lafiya, hotuna ne na gaske.

    Aung San Suu Kyi mai shekara 81 na tsare tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi, inda suka hamɓarar da gwamnatinta shekaru biyar da suka gabata.

  7. Kullen Allah ta yi Allah wadai da haren-haren ƴanbindiga a arewacin Najeriya

    Kungiyar Kullen Allah

    Asalin hoton, Kullen Allah

    Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta Kullen Allah a Najeriya (KACRAN) ta yi Allah wadai da hare-haren da 'yan bindiga suka kai a jihohin Zamfara, Sokoto da Katsina, inda aka kashe mutane, aka ƙone wasu da ransu, tare da yin garkuwa da mutane da dama.

    A cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar na ƙasa, Khalil Mohd Bello ya sanya wa hannu, KACRAN ta bayyana hare-haren a matsayin rashin Imani, kuma barazana ga zaman lafiyar al'umma da wadatar abinci a Najeriya.

    Ƙungiyar ta yi kira ga 'ƴan bindiga su dakatar da kashe-kashe da garkuwa da mutane tare da sakin waɗanda suke tsare da su ba tare da wani sharaɗi ba.

    Haka kuma ta roƙi ƙungiyoyin sa-kai da su guji kai hare-hare ko kashe makiyaya marasa laifi, tana mai cewa ba kowane Bafulatani ba ne ɗan bindiga.

    KACRAN ta kuma yi kira ga shugabannin Arewa, ciki har da 'yan siyasa da sarakuna da malamai da manoma da makiyaya da su haɗa kai wajen kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta addabi yankin.

    A ƙarshe, ƙungiyar ta buƙaci gwamnatin tarayya ta ɗauki tsarin zaman lafiya ta gabatar, wanda ya haɗa da tattaunawa, kare gonaki da hanyoyin kiwo, da kuma lalubo hanyoyin kwance damarar 'yan bindiga domin dawo da zaman lafiya a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya.

  8. Waɗanda ke jiran hukunci kisa a Saudiyya sun kira BBC ta waya

    BBC

    Akwai tsananin damuwa a muryar wani matashi dan kasar Habasha lokacin da ya samu damar tuntubar BBC ta wata wayar da ke cikin ɗakinsa a gidan yarin da ake tsare da masu jiran hukuncin kisa a Saudiyya.

    Habtom, wanda aka sauya sunansa domin kare martabarsa kamar yadda aka yi wa ɗayan fursunan da aka ambata a wannan rahoto, ya shafe fiye da shekara uku ana tsare da shi a wani gidan yari da ke birnin Khamis Mushait da ke kudancin Saudiyya.

    Duk da hayaniyar fursunonin da ke tare da shi suna ta ihun magana a bayansa, ya roƙi a taimaka masa, kuma ana iya jin ɓacin ransa ganin yadda gwamnatinsa ke nuna kamar ba ta ɗaukar wani mataki don sauya makomarsa ba.

    Shi da wasu daga cikin takwarorinsa fursunoni sun tsere daga yaƙi da talauci a ƙasarsu, da fatan samun rayuwa mafi kyau.

  9. Yawan mazan da ke ɗaukar hutun haihuwa a Japan ya ƙaru da kashi 50

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Yawan maza da ke ɗaukar hutun haihuwa a Japan ya ƙaru zuwa sama da kashi hamsin a karon farko, yayin da halayen da ake nunawa ga aiki ke ci gaba da canzawa.

    Ma'aikatar ƙwadago a Japan ta ce adadin ya ƙaru da kashi goma a bara inda ya aka ga fiye da rabin maza ma'aikata sun ɗauki hutun haihuwa.

    Tsawon shekaru dai gwamnatin Japan na ƙarfafa gwiwar iyaye maza su ɗauki domin su je su yi raino, inda ta ɓullo da ɗumbin matakan tallafi.

    Manufar hakan ita ce shawo kan daɗaɗɗiyar al'adar wuraren aiki a Japan inda maza ke jin suna cikin matsin lamba ta su yi aikin sa'o'i da yawa kuma cikin fargabar cewa ɗaukan hutu zai ɓarar musu da damar samun ƙarin girma.

  10. Yadda ƴan Najeriya ke sahun tattakin ranar Arbaeen a birnin Karbala na Iraq

    A ranar 20 ga watan Safar na kowane wata ne mabiya mazahabar Shi'a daga ko'ina a faɗin duniya ke tattaki na jimamin kisan jikan manzon Allah SAW, Imam Hussain, a birnin Karbala na ƙasar Iraq.

    Taron wanda ake yi wa laƙabi da "Tattakin Arbaeen" kuma ake yin sa ranar 20 ga watan Safar ya kasance cikar kwana 40 tun bayan kisan Imam Hussain ranar 10 ga watan Muharram.

    ....

    Asalin hoton, Ismaeel Albabawee

    ..

    Asalin hoton, Isma'eel Albabawee

    ....

    Asalin hoton, Ismaeel Albabawee

    To sai dai tattakin na farawa ne da yammacin ranar 19 ga wata inda kowace tawaga kan shiga hubbare ko kuma "haramin" Imam Hussain da na ɗan uwansa Abul Abbas domin jaje da addu'o'i.

    ...

    Asalin hoton, Ismaeel Albabawee

    Taron na Arbaeen shi ne taro na biyu mafi girma a duniya bayan wani taron Maha Kumbh Mela na mabiya addinin Hindi.

    ...

    Asalin hoton, Ismaeel Albabawee

    Alƙaluma daga Karbala sun nuna cewa mutum miliyan 20 zuwa 30 ke halartar wannan alhini a duk ranar 20 ga watan Safar - wata na biyu a addinin Musulunci, a kowace shekara.

    ....

    Asalin hoton, Ismaeel Albabawee

    ..

    Asalin hoton, Isma'eel Albabawee

    ..

    Asalin hoton, Isma'eel Albabawee

    ..

    Asalin hoton, Isma'eel Albabawee

    ..

    Asalin hoton, Isma'eel Albabawee

    ..

    Asalin hoton, Isma'eel Albabawee

    ..

    Asalin hoton, Isma'eel Albabawee

    ..

    Asalin hoton, Isma'eel Albabawee

  11. Sanata Rufai Hanga ya fice daga jam'iyyar NDC ta su Kwankwaso

    ...

    Asalin hoton, Umar Saminu Mai-Adashi/FB

    Sanata Rufai Hanga mai wakiltar Kano ta Tsakiya a Majalisar Dattawa ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar NDC, jam’iyyar tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.

    A cikin wasiƙar murabus da ya aike wa shugabannin jam’iyyar a ranar 3 ga Agustan 2026, Sanata Hanga ya ce ya yanke shawarar barin jam’iyyar ne bayan yin nazari da dogon tunani kan makomarsa ta siyasa

    Sanatan ya kuma gode wa shugabannin jam’iyyar da mambobinta a mazabar Dakata da ke ƙaramar hukumar Nasarawa a Kano bisa goyon baya da haɗin kan da suka nuna masa a lokacin da yake cikinta.

    Haka kuma ya ce ya miƙa katin shaidar kasancewarsa ɗan jam’iyyar tare da neman a cire sunansa daga rajistar mambobin NDC a matakin mazaba, yana mai yi wa jam’iyyar da magoya bayanta fatan alheri a nan gaba.

  12. Iran ta ce ta harbo jirgin yaƙin Amurka mara matuƙi a mashigar Hormuz

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar juyin juya halin Iran (IRGC) ta ce ta harbo wani jirgin yaƙin Amurka mara matuƙi kirar MQ-9 a sararin mashigar Hormuz.

    A cikin wata sanarwa, rundunar ta ce ta harbo jirgin ne da wani sabon makami da rundunar ta ƙera.

    Sai dai sanarwar ba ta bayyana ranar ko lokacin da aka harbo jirgin ba.

    Har zuwa yanzu, rundunar sojin Amurka ta CENTCOM ba ta tabbatar ko musanta rahoton ba.

  13. 'Yanbindiga sun kashe mutum 18 ciki harda sojoji huɗu a Zamfara da Sokoto

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Aƙalla mutum 18, ciki har da sojoji huɗu ne suka mutu bayan wasu 'yanbindiga sun kai hare-hare a wasu al'ummomi da ke jihohin Zamfara da Sakkwato a arewa maso yammacin Najeriya.

    A jihar Zamfara, mazauna Kasuwar Daji sun ce maharan sun mamaye wani sansanin sojoji kafin su yi garkuwa da fiye da mutum 100 daga ƙauyen.

    Rahotanni sun ce daga baya maharan sun saki matan da suka kama, amma har yanzu suna riƙe da kusan maza 52.

    A jihar Sakkwato kuwa, an ce 'yanbindigar sun shafe sa'o'i suna kai hare-hare gida-gida a ƙauyen Lajinge da ke ƙaramar hukumar Sabon Birni, inda suka kashe fararen hula, suka sace dabbobi tare da ƙone wani gida.

    Daga cikin waɗanda aka kashe akwai wani magidanci da 'ya'yansa maza biyu da aka ce sun ƙone da ransu yayin da suke ɓoye a cikin gida.

    Shaidu sun kuma ce an yi garkuwa da wasu mata biyu, yayin da har yanzu hukumomi ba su fitar da bayaninsu kan hare-haren ba.

  14. Majalisar masana ta Iran ta yi gargaɗi kan yarda da Amurka

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar Masana ta Iran ta yi gargaɗi game da amincewa da Amurka, tana mai cewa abubuwan da suka faru a baya-bayan nan sun nuna cewa dogaro da Washington ko fatan cimma yarjejeniya da ita ba zai haifar da sakamako mai kyau ba.

    A cikin wata sanarwa, majalisar ta ce karya alkawuran da Amurka ta yi ya nuna cewa amincewa da ita "mafarki ne marar tushe"

    Majalisar ta kuma ce duk wani kira na sassautawa ko mika wuya da sunan kare zaman lafiya cin amana ne da bai kamata a amince da shi ba.

    Ta jaddada cewa duk wani mataki da Iran za ta ɗauka dole ne ya kasance daidai da umarni da jagorancin Jagoran Ƙolin ƙasar, Mojtaba Khamenei.

  15. An saki alƙalin babbar kotun Kebbi da aka sace

    An saki alƙalin babbar kotun jihar Kebbi, Justice Faruku Bunza, wanda aka yi garkuwa da shi mako guda da ya wuce a ƙaramar hukumar Bunza.

    A cikin wata sanarwar da rundunar ’yan sandan jihar Kebbi ta fitar, mai magana da yawunta Bashir Usman ya ce an tabbatar da sakin alkalin a ranar Litinin, inda iyalansa da ma’aikatar shari’a ta jihar suka tabbatar da komawarsa gida cikin ƙoshin lafiya.

    Rundunar ta ce duk da cewa masu garkuwar sun nemi kuɗin fansa, ba a biya su ko sisi ba kafin sakin alkalin.

    Ta kuma bayyana cewa jami’an tsaro na ci gaba da bincike domin gano tare da kama mutanen da ke da hannu a sace alkalin domin su fuskanci hukunci a gaban doka.

  16. Jami’in soja da ɗansanda sun mutu yayin daƙile harin ’yanbindiga a zamfara

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Najeriya ta ce wani jami’inta da ɗansanda sun rasa rayukansu yayin da suke daƙile wani hari da ’yanbindiga suka kai sansanin sojoji da ke Kasuwan Daji a ƙaramar hukumar Kaura Namoda ta jihar Zamfara.

    Rundunar Operation FANSAN YAMMA ta ce maharan sun yi ƙoƙarin kutsawa cikin sansanin da misalin ƙarfe 1:40 na safiyar ranar 2 ga Agusta, amma dakarun da ke wurin sun gano yunƙurin da wuri tare da mayar da martani, lamarin da ya tilasta wa maharan tserewa.

    Bayan artabun, ƙarin dakaru sun bi sahun maharan, inda suka samu nasarar kuɓutar da mutum tara daga cikin mutanen da aka yi garkuwa da su a lokacin harin.

    Rundunar ta kuma ce sojoji biyu sun jikkata sakamakon harbin bindiga kuma an garzaya da su asibiti domin samun kulawa.

    Rundunar ta kuma ƙaryata rahotannin da ke cewa jami’an tsaro shida ne suka mutu, tana mai jaddada cewa jami’in soja ɗaya da ɗansanda ɗaya ne suka rasa rayukansu.

  17. Iran ta ce ba ta wata tattaunawa da Amurka a halin yanzu

    ...

    Asalin hoton, Tasnim news agency

    Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya ce a halin yanzu babu wata tattaunawa da ke gudana tsakanin Iran da Amurka, duk da cewa Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa za a fara sabbin tattaunawa a yau Litinin.

    Baghaei ya bayyana cewa a yanzu Tehran ta fi mayar da hankali kan tattaunawar da take yi da Oman game da mashigar Hormuz, wadda ta shafe kwanaki takwas tana gudana.

    Ya ce duk wata fahimta da ake samu da Oman ba tana nufin an buɗe mashigin Hormuz ba har sai an tabbatar da tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin.

    Baghaei ya kuma jaddada cewa rufe mashigin Hormuz ya biyo bayan hare-haren Amurka da Isra'ila ne, ba saboda saɓani tsakanin Iran da Oman ba.

    A cewarsa, Iran da Oman na tattaunawa kan wata sabuwar hanyar zirga-zirgar jiragen ruwa.

  18. Iran ta zartar da hukuncin kisa kan wasu da take zargi da yi wa Isra'ila leƙen asiri

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar shari’ar Iran ta sanar da aiwatar da hukuncin kisa kan Omid Behzad da Pouria Safvat a safiyar Litinin, bayan kotu ta same su da laifin yi wa Isra’ila leƙen asiri.

    A cewar kamfanin yaɗa labaran ma’aikatar shari’ar Iran, Mizan, mutanen biyu sun kasance suna tattarawa tare da aika wa hukumar leƙen asirin Isra’ila ta Mossad bayanai, hotuna da kuma bayanan wuraren da cibiyoyin soji da na tsaro na Iran suke.

    Mahukuntan Iran sun ce irin waɗannan bayanai sun taimaka wajen gudanar da ayyukan leƙen asiri da suka shafi tsaron ƙasar.

    Sai dai ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama da wasu lauyoyi sun dade suna nuna damuwa kan yadda ake gudanar da irin waɗannan shari’o’i a Iran, suna zargin cewa ana gaggauta aiwatar da hukuncin kisa ba tare da tabbatar da cikakken tsarin shari’a mai adalci ba.

    Sun kuma ce rashin bai wa waɗanda ake tuhuma damar samun lauya yadda ya kamata na daga cikin matsalolin da ke haifar da tambayoyi kan adalcin irin waɗannan hukunci.

  19. Iran na ƙarfafa hulɗa da Saudiyya da Pakistan kafin tattaunawarta da Amurka

    ....

    Asalin hoton, IRNA

    Iran na ci gaba da ƙarfafa hulɗarta da Saudiyya da Pakistan ta hanyar tattaunawa da manyan jami'an ƙasashen biyu, a daidai lokacin da ake sa ran fara sabon zagayen tattaunawa tsakanin Tehran da Washington cikin sa'o'i masu zuwa.

    Kamfanin dillancin labaran gwamnatin Iran (IRNA) ya ruwaito cewa ministan harkokin wajen ƙasar, Abbas Araqchi, ya yi tattaunawa ta biyu a ranar Lahadi da takwaransa na Saudiyya, Faisal bin Farhan Al Saud.

    Haka kuma ya yi wata tattaunawa ta wayar tarho da ministan harkokin wajen Pakistan, sannan daga bisani ya tuntubi shugaban rundunar sojin Pakistan, Field Marshal Asim Munir, wanda ake kallon sa a matsayin ɗaya daga cikin manyan masu tasiri a harkokin tsaro da siyasar ƙasar.

    Wadannan tattaunawa na zuwa ne bayan shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa za a fara sabon zagayen tattaunawa tsakanin Amurka da Iran, inda za a mayar da hankali kan batutuwan mashigin ruwa na Hormuz da kuma shirin nukiliyar Iran.

  20. Trump ya sanar da fara sabbin tattaunawa da Iran a yau Litinin

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa za a fara sabbin tattaunawa tsakanin Amurka da Iran a yau Litinin, bayan sanarwar da ya yi a daren jiya game da janye wasu hare-haren da aka shirya kai wa Iran.

    Trump ya ce a halin yanzu akwai fahimta kan batun mashigar Hormuz, kuma yana da yakinin cewa za a cimma yarjejeniya kan shirin nukiliyar Iran.

    Trump ta fadi hakan ne yayin da yake magana da manema labarai a cikin jirgin shugaban ƙasa na Air Force One a ranar Lahadi.

    A gefe guda kuma, ministocin harkokin wajen Iran, Saudiyya, Pakistan, Qatar da Jordan na ci gaba da gudanar da tattaunawa da shawarwari, waɗanda ake ganin sun fi mayar da hankali kan tattaunawar da ke tsakanin Tehran da Washington.