Alhakin rufe mashigar Hormuz ya kan Amurka - Iran
Iran ta ce ya kamata ƙasashen duniya da su ɗora wa Amurka alhakin duk wata illa ta tsaro da tattalin arziki da ka iya tasowa sakamakon toshe tasoshin ruwanta a mashigar Hormuz.
Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ne ya bayyana hakan a wata tattaunawar waya da takwaransa na Jamus, Johann Wadephul, inda ya ce matakan da Amurka ke ɗauka a yankin ne suka haddasa rashin tsaro a mashigar.
Araqchi ya ce Iran na ci gaba da tattaunawa da Oman domin nemo wata amintacciyar hanyar zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar Hormuz.
Ya kuma zargi Amurka da Isra'ila da haddasa rashin kwanciyar hankali a yankin ta hanyar hare-haren soji da yake cewa suna kai wa Iran.
A cewar kafafen yaɗa labaran Iran, ministan ya jaddada cewa samar da tsaro a mashigar Hormuz na bukatar kawo ƙarshen abin da ya kira matakan tsoma bakin Amurka ba bisa ƙa'ida ba, ciki har da toshe zirga-zirgar jiragen ruwa da sauran ayyukan da ya ce sun saɓa wa alƙawurran ƙasar.