Alhakin rufe mashigar Hormuz ya kan Amurka - Iran

Asalin hoton, Getty Images
Iran ta ce ya kamata ƙasashen duniya da su ɗora wa Amurka alhakin duk wata illa ta tsaro da tattalin arziki da ka iya tasowa sakamakon toshe tasoshin ruwanta a mashigar Hormuz.
Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ne ya bayyana hakan a wata tattaunawar waya da takwaransa na Jamus, Johann Wadephul, inda ya ce matakan da Amurka ke ɗauka a yankin ne suka haddasa rashin tsaro a mashigar.
Araqchi ya ce Iran na ci gaba da tattaunawa da Oman domin nemo wata amintacciyar hanyar zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar Hormuz.
Ya kuma zargi Amurka da Isra'ila da haddasa rashin kwanciyar hankali a yankin ta hanyar hare-haren soji da yake cewa suna kai wa Iran.
A cewar kafafen yaɗa labaran Iran, ministan ya jaddada cewa samar da tsaro a mashigar Hormuz na bukatar kawo ƙarshen abin da ya kira matakan tsoma bakin Amurka ba bisa ƙa'ida ba, ciki har da toshe zirga-zirgar jiragen ruwa da sauran ayyukan da ya ce sun saɓa wa alƙawurran ƙasar.
















