Kocin ƙwallon ƙafar Koriya ta Kudu ya yi murabus bayan rashin nasara a gasar cin kofin duniya
Hong Myung-bo ya yi murabus daga muƙaminsa na kocin tawagar ƙwallon ƙafar ƙasar Koriya ta Kudu bayan da suka kasa tsallakewa zuwa zagayen gaba na gasar cin kofin duniya. \
Ƙungiyar ta yi fatan za ta iya tsallakewa zuwa zagaye na gaba a gasar a matsayin ɗaya daga ƙasashe takwas na alfarma, amma hakan ya ci tura ranar Asabar.
Ficewar da wuri ya haifar da suka a gida, inda shugaban ƙasar Lee Jae Myung ya yi kira da a gudanar da bincike kan dalilan da suka sa tawagar ta kasa taka rawar gani.
Hong ya nemi afuwar magoya bayansa ranar Lahadi kuma ya ce alhakin "ya rataya ne a wuya ta ni kaɗai a matsayina na kociyan ƙungiyar".
Koriya ta Kudu wadda ke matsayi na 32 a jerin ƙasashen da suka fi hazaƙa a fagen ƙwallon ƙafa, ta ci wasa ɗaya da kuma sha kashi a wsanni biyu a gasar cin kofin duniya ta, inda ta ƙare a bayan Mexico da Afrika ta Kudu, wadanda ke matsayi na 15 da 60 a duniya.