KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a ranar Asabar 12/09/2026

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Adeyemi Adeniyi
  • Abdourahamane Tchiani
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. Wani samfurin AI ya kauce wa matakan kariya tare da yin kutse

    Open AI

    Asalin hoton, Getty Images

    Kamfanin kirkirarriyar basira - na OpenAI ya tabbatar da wani cewa wasu samfuransa, na AI din sun kauce wa wasu matakan kariya inda suka je suka yi kutse domin kai hari kan wani shafin intanet.

    OpenAI ya ce samfuransa da yake gwadawa sun kai hari kan wata manhaja mai suna RubyGems a watan Mayu, wata biyu kafin harin da ya yi fice kan shafin Hugging Face.

    Kamfanin na OpenAI ya ce a kutsen abin da samfuran nasa suka yi ba wani mai illa ba ne, sun dai tattaro bayanan da aka riga aka sani ne.

    Sai dai masu gudanar da RubyGems sun ce lamarin ya tilasta musu dakatar da bude sababbin shafuka na wani dan lokaci domin tabbatar da tsaro.

    Wannan sabon rahoto na kara nuna damuwa da fargabar da ake yi cewa fa, idan har ba a gaggauta daukar matakai ba to fa kirkirarriyar basira ta AI - ka iya kaiwa matakin da dan'Adam ba zai iya sarrafa ta ba.

  2. Saudiyya ta rufe muhimmin bututun mai bayan hari daga Iraq

    Bututun Aramco

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni sun ce Saudiyya ta rufe wani muhimmin bututun mai da ake tura danyen mai zuwa gabar Tekun Bahar Maliya, ta cikinsa - wanda ke ba da damar kauce wa amfani da Mashigar ruwa ta Hormuz, bayan wani hari da jirage marasa matuka suka kai masa daga cikin Iraki.

    Wakilin BBC ya ce bututun na samar da kashi hudu ko biyar na man duniya a watannin nan.

    Gwamnatin Saudiyya ba ta bayyana wadanda ke da alhakin harin ba, amma ta ce irin wadannan hare-hare a baya suna da alaka da kungiyoyin da ke samun goyon bayan Iran.

    Lamarin na zuwa ne yayin da kungiyar Houthi da ke kawance da Iran ta ce ta kwace iko da daukacin gabar tekun Bahar Maliya ta Yemen, lamarin da ke kara karfafa matsayinta a wata muhimmiyar hanyar safarar kayayyaki ta ruwa.

    Kungiyar ta Houthi ta kuma ce za ta hana zirga-zirgar jiragen ruwa na Saudiyya a Mashigar Bab al-Mandab, abin da zai kara matsin lamba kan kasuwar man fetur ta duniya - inda samar da man zai kara raguwa.

  3. Farawa

    Masu bibiyarmu a wannan shafi na kai tsaye daga BBC Hausa muna muku barka da safiyar ta Juma'atu babbar rana.

    Za ku iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin kallon wasu hotuna da bidiyon hirarraki da muke wallafawa tare da yin tsokaci a kai.