KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 15/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 15 ga watan Yunin 2026.

Skip Bidiyo and continue reading
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Kutama
  • xxx
  • XXX
  • Sadis Buba
  • Pantami
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Usman MINJIBIR

  1. Birtaniya, Faransa, Jamus da Italiya sun yi maraba da yarjejeniyar Iran da Amurka

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Birtaniya, da Faransa, da Jamus da Italiya sun fitar da sanarwar haɗin gwiwa inda suka yi maraba da yarjejeniyar, suna masu cewa sake buɗe mashigar Hormuz abu ne mai matuƙar muhimmanci.

    Sanarwar ta kuma jaddada cewa bai kamata Iran ta taɓa mallakar makamin nukiliya ba.

    Kasashen huɗu na Turai sun ce a shirye suke su ɗage takunkuman da suka sanya wa Iran din idan har ta ɗauki matakai bayyanannu da za su ba da damar bibiyar shirinta na makamashin nukiliya don tabbatar da cewa ba ta sauka daga layi ba.

  2. Iran da Amurka za su rattaɓa hannu kan yarjejeniya ranar Juma'a a Switzerland

    .....

    Asalin hoton, BBC collage/getty/IRNA

    Iran da Amurka sun sanar da cewa sun cimma wata yarjejeniyar fahimtar juna domin kawo ƙarshen yaƙin da ke tsakaninsu, bayan watanni na rikici da tattaunawa.

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana a wani saƙo cewa yarjejeniya da Iran “ta kammala gaba ɗaya,” yana mai taya kowa murna kan wannan ci gaba.

    Shi ma firaministan Pakistan, Shahbaz Sharif, ya sanar cewa an cimma wannan yarjejeniya, tare da ƙara da cewa za a yi bikin rattaba hannu a hukumance ranar Juma’a, 19 ga watan Yuni, a ƙasar Switzerland.

    Haka zalika, Majalisar Tsaron Ƙasa ta Iran ta tabbatar da cewa an cimma wannan yarjejeniyar fahimtar juna da nufin kawo ƙarshen yaƙin da aka ɗauki watanni ana yi inda ta ce za a dakatar da dukkan ayyukan soja nan take a dukkan wurare.

    Wannan yarjejeniya na daga cikin manyan matakai da ake ganin za su iya rage tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya tare da buɗe hanya ga zaman lafiya mai ɗorewa.

  3. Assalamu alaikum

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za kuma ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.