KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Juma'a 14/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Juma'a 14/08/2026

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Yariman Saudiyya ya gana da kwamandan CENTCOM a Jeddah

    Hoton Yaraiman Saudiyya

    Asalin hoton, Reuters

    Kamfanin Dillancin Labaran Saudiyya ya ruwaito cewa Yarima Mai Jiran Gado na Saudiyya, Mohammed bin Salman, ya gana da Brad Cooper, kwamandan rundunar CENTCOM ta sojojin Amurka da ke Gabas ta Tsakiya.

    Jagororin biyu sun tattauna kan haɗin gwiwar tsaro tsakanin Saudiyya da Amurka.

    Bin Salman da Mista Cooper sun kuma tattauna kan halin da yankin Gabas ta Tsakiya ke ciki a halin yanzu, da kuma ƙoƙarin rage tashin hankali tare da ƙarfafa tsaro da zaman lafiya a yankin, kamar yadda kamfanin dillancin labaran ƙasar ya bayyana.

    A cikin makonnin da suka gabata, bayan hare-haren da aka kai kan Saudiyya, ƙasar tare da Amurka sun ƙaddamar da hare-haren haɗin giwar soji kan ƙungiyoyin mayaƙa masu alaƙa da Iran a Iraƙi.

  2. Me ke faruwa a mashigar Hormuz yayin kokawar iko da ita?

    Mashigar Hormuz

    Asalin hoton, Reuters

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa har yanzu akwai taƙaitar zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar Hormuz, yayain da rikici kan ikon mashigar ke ƙara tsananta tsakanin Amurka da Iran.

    Alƙaluma daga kamfanin sanya idanu kan zirga-zirgar jiragen ruwa na Kepler sun nuna cewa jiragen ruwan da suka ratsa ta mashigar a ranar Alhamis ya ɗan ƙaru kaɗan kan jirage 12 da su bi ta mashigar a ranar Laraba.

    Kididdigar Kepler ta nuna cewa jirage tara ne suka ratsa mashigin a jiya Alhamis, idan aka kwatanta da jirage biyar da suka ratsa a ranar Laraba.

    Daga cikin waɗannan, jirage biyar sun shiga Tekun Fasha, yayin da huɗu suka fita zuwa Tekun Oman, kuma mafi yawansu sun bi hanyar jiragen ruwa ta Iran.

  3. Amurka ta yi barazanar mayar da Iran saniyar ware a duniya

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Sakataren Baitul-malin Amurka, Scott Bessent ya yi barazanar mayar da Iran saniyar ware a fannin tattalin arziki, irin wanda duniya ba ta taɓa gani ba.

    Bai yi ƙarin bayani game da batun ba, amma ya ce za a iya sanar da sabbin matakai kan Iran a mako mai zuwa.

    Sakataren Tsaro Pete Hegseth ya bayyana cewa Amurka a shirye take ta ci gaba da rufe wa Iran hanyoyin ruwa na tsawon lokaci.

    Iran ta ci gaba da riƙe ikon Mashigin Hormuz.

    Hadaddiyar Daular Larabawa ta bayar da rahoton harin da Iran ta kaiwa wasu jiragen dakon mai biyu.

  4. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Juma'a, Haji babbar rana, kamar yadda Hausawa ke yi mata kirari.

    Yau ma kamar jiya, Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniyar ke ciki.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.