Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 28/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 28/06/2026.

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. An kama jami’an gwamnatin Iraq 47 bisa zargin rashawa

    Hukumomin tsaro a ƙasar Iraq sun kama jami’an gwamnati da ƴan siyasa 47, ciki har da ‘yan majalisar dokoki, a wani samame da suka kai domin yaƙi da rashawa.

    An gudanar da wannan farmaki ne a yankin Green Zone da ke Baghdad, wurin da ake tsaurara tsaro sosai a babban birnin ƙasar.

    Rahotanni sun ce wannan mataki na daga cikin sabuwar ƙudirin yaƙi da rashawa da firaministan ƙasar Iraq na yanzu, Ali Zaidi ke jagoranta.

    Tun da farko ma an kama mataimakin ministan man fetur, Adnan Jalili.

    Wani jami’i a gwamnatin Iraq da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida cewa ana zargin waɗanda aka kama da laifuka ciki har da wawure dukiyar gwamnati da safarar dala da kuma man fetur ba bisa ƙa’ida ba.

  2. Gwamnatin Oyo ta ɗage dokar hana fita da ta saka wa ƙananan hukumomi 10

    Gwamnatin Jihar Oyo ta sanar da ɗage dokar hana fita da ta sanya a ƙananan hukumomi 10, biyo bayan sace mutanen da aka yi a yankin Oriire.

    Tun farko gwamnati ta saka dokar hana fita na sa'o'i 16 kafin daga bisani ta ƙara wani yini, domin daƙile matsalolin tsaro a yankin.

    A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Watsa Labarai, Prince Dotun Oyelade ya fitar, ya ce yanzu mazauna yankunan da abin ya shafa za su iya komawa gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

    Haka kuma ya gode musu kan haɗin kai da fahimtar juna da suka nuna a lokacin da dokar ke aiki.

    Oyelade ya ƙara da cewa gwamnati na ci gaba da sanya ido kan al’amuran tsaro a yankin, tare da tabbatar wa al’umma cewa ana ƙoƙarin ganin an shawo kan lamarin sace mutanen.

    Lamarin sace mutanen ya faru ne a ranar 15 ga Mayu, lokacin da wasu ‘yanbindiga suka kai hari makarantu uku a yankin Oriire, inda suka sace ɗalibai da malamai har 45. Bayan wasu kwanaki, rahotanni sun nuna cewa ɗaya daga cikin malaman da aka sace, wanda ke koyar da lissafi, ya mutu a hannun maharan.

  3. Jirgin Faransa ya ratsa mashigar Hormuz da izinin Iran

    Wani jirgin ruwa mallakin wani kamfanin Faransa ya tsallaka mashigar Hormuz da izinin Iran, inda aka kuma tabbatar da cewa ya wuce cikin aminci ba tare da wata matsala ba.

    Rahotanni sun nuna cewa jirgin ya tashi ne daga kusa da Dubai a Hadaddiyar Daular Larabawa, kafin ya bi mashigar Hormuz zuwa gabar tekun Oman, inda yake a halin yanzu.

    Sai dai har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanai kan yadda aka tsara wannan wucewar ba ko irin tsarin tsaron da aka tanada ba, duk da cewa kamfanin na da sauran jiragen ruwansa guda 10 a yankin Tekun Farisa.

    Ministan sufuri na Faransa, Philippe Tabaro, ya yaba da wannan izini da Iran ta bayar, yana mai cewa jirgin na ɗauke da tutar Faransa kuma ma’aikatansa ‘yan ƙasar Faransa ne.

    A gefe guda kuma, ƙasar Oman ta sanar da kirkirar wata hanya da za a bi a gaar tekunta, sai dai Iran ta jaddada cewa hanyarta ce kaɗai mai aminci, tare da gargaɗin cewa za ta ɗauki mataki kan duk wanda ya karya wannan umarni.

  4. An kashe sojan Isra'ila yayin artabu a Kudancin Lebanon

    Sojojin Isra’ila sun sanar a ranar Lahadi cewa ɗaya daga cikin sojojinsu ya mutu yayin artabu a kudancin Lebanon, kwanaki biyu kacal bayan Isra’ila da Lebanon sun rattaɓa hannu kan wata yarjejeniya da ke nufin kawo ƙarshen rikicin.

    Wata sanarwa daga jami’an sojin ta bayyana cewa mamacin, Kyaftin David Hazot Nezami mai shekaru 21, wanda ke jagorantar runduna, ya mutu ne lokacin da sojojin suka yi arangama da ƙungiyar Hezbollah a yankin Deir Saryan.

    Rahoton ya kuma ce wasu daga cikin sojojin Isra’ila sun samu raunuka sakamakon arangamar.

    A gefe guda kuma, kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Lebanon ta ruwaito cewa Isra’ila ta kai wani hari ta sama a wajen garuruwan Deir Ezzor da Tayyiba a kudancin ƙasar.

    Tun bayan ɓarkewar rikicin Isra’ila da Hezbollah a farkon watan Maris, an tabbatar da mutuwar sojojin Isra’ila 38 da kuma farar hula ɗaya da ke aiki tare da su.

  5. Atiku ya zargi shirin raunana ƴan adawa saboda hukuncin kotu kan jam'iyyar NDC

    Tsohon mataimakin shugaban ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya yi allawadai da abin da ya kira yunƙurin daƙile rajistar jam’iyyar NDC, yana mai zargin cewa hakan wani yunƙuri ne na karkatar da Najeriya zuwa tsarin jam’iyya daya ƙarkashin Shugaba Bola Tinubu.

    Atiku ya yi wannan martani ne bayan wata kotun tarayya da ke Lokoja jihar Kogi ta soke hukuncinta na ranar 10 ga Disamba 2025 wanda ya bai wa hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) umurnin yi wa NDC rajista a matsayin jam’iyya.

    Mai shari’a Isah Dashen ya ce ya kamata a shigar da jam’iyyar PMP a cikin ƙarar, domin shari’ar ta shafi muradunta.

    A cikin wata sanarwa da ofishin yaɗa labaran Atiku ya fitar, ya ce bai yi mamakin wannan hukunci ba, yana mai gargaɗin cewa idan aka ci gaba da abin da ya kira shirin raunana ‘yan adawa domin bai wa Tinubu damar sake tsayawa takara a 2027, hakan na iya janyo mummunan sakamako ga dimokuraɗiyya.

    Ya ƙara da cewa shiga cikin zaɓuɓɓuka ginshiƙin dimokuradiyya ne, kuma duk wani yunƙuri na hana ‘yan kasa ‘yancin zaɓe na iya jawo “rikici da tarzoma.”

    Haka kuma ya buƙaci ɓangaren shari’a su kiyaye mutuncinsu tare da kauce wa shiga siyasa, yana mai cewa kotuna su ne mafakar talakawa, don haka bai kamata a lalata amincinsu ba.

  6. Duk wani katsalandan ga ikon ƙasarmu a mashigar Hormuz zai ƙara tsananta rikici ne - Iran

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, ya yi gargaɗin cewa duk wani yunƙuri na katsalandan a yadda Iran ke tafiyar da mashigar Hormuz zai ƙara tsananta rikici a yankin.

    Araqchi, wanda ke ziyara a birnin Baghdad, ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai tare da takwaransa na Iraq, inda ya ce bisa fahimtar juna tsakanin Iran da Amurka, za a dawo da zirga-zirgar mashigar cikin kwanaki 30, a ƙarƙashin cikakken ikon Iran kaɗai.

    Ya jaddada cewa Iran ce ke da alhakin aiwatar da wannan tsari, yana mai cewa duk wani ƙoƙari na ƙirƙirar wata hanya dabam ko tsoma baki daga waje zai janyo tsaiko da kuma ƙarin rikice-rikice, wanda a cewarsa tuni an fara gani a abubuwan da suka faru cikin dare biyu a yankin.

    A cikin kwanaki uku da suka gabata, an kai hari kan aƙalla jiragen ruwa biyu da ke wucewa mashigar Hormuz, lamarin da ya haddasa musayar wuta tsakanin Iran da Amurka, inda kowanne ɓangare ke zargin ɗaya da karya yarjejeniyar tsagaita wuta..

  7. Gwamnan Benue ya umarci a fara bincike kan kisan shugaban makiyaya

    Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, ya umarci hukumomin tsaro da su fara bincike nan take kan kisan shugaban ƙungiyar makiyaya ta MACBAN a jihar, Alhaji Ardo Risku, tare da abokinsa.

    Ya bayyana matuƙar kaɗuwarsa da alhini kan lamarin, yana mai cewa ya zo ne a wani lokaci da jihar ke fara samun zaman lafiya a yankuna daban-daban.

    Gwamnan ya ce wannan kisan ba wai kawai abin takaici ba ne, har ma wata ƙoƙari ce ta karya zaman lafiya da sulhun da gwamnatinsa ke ƙoƙarin tabbatarwa, musamman ganin cewa ya faru ne jim kaɗan bayan wani muhimmin taron tsaro.

    Saboda haka ya buƙaci a gudanar da bincike mai zurfi da gaskiya, tare da kamo waɗanda suka aikata laifin domin gurfanar da su a gaban shari’a

    Haka kuma ya yi kira ga al’umma su kwantar da hankalinsu, yana mai gargaɗin cewa bai kamata a bari masu anfani da rikici su tayar da tarzoma ba, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan.

  8. Adadin waɗanda suka mutu a girgizar ƙasar Venezuela ya haura 1,400

    Adadin waɗanda suka mutu a girgizar ƙasa mai ƙarfi guda biyu da suka afkawa ƙasar Venezuela ya haura 1,400, yayin da har yanzu ake ci gaba da ayyukan ceto.

    Kwana uku bayan afkuwar girgizar, ana neman mutane da dama da suka ɓace, yayin da jami’an agaji ke ci gaba da tono waɗanda suka maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzai.

    A lokaci guda, ƙorafe-ƙorafen jama’a na ƙaruwa kan yadda gwamnati ke tafiyar da lamarin.

    Wakilin BBC da ke garin La Guaira, wanda ya fi fuskantar iftila’in, ya ce halin da ake ciki na da matuƙar tsanani, inda har yanzu ba a san adadin mutanen da ke maƙale a ƙarƙashin gine-ginen da suka rufta ba.

    Ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa sun isa yankin, inda ƙungiyoyi daga ƙasashen Mexico, Brazil, da sauransu ke aiki ba dare ba rana wajen ceto da taimakawa waɗanda bala’in ya shafa.

  9. 'Wani jami'in Amurka ya tabbatar da harin Iran kan wuraren sojin ƙasar'

    Kamfanin dillancin labaran Reuters ya rawaito cewa wani jami’in Amurka ya tabbatar da cewa Iran ta harba makamai masu linzami da kuma jiragen sama marasa matuƙa zuwa wasu ƙasashe makwabta, ciki har da Bahrain da Kuwait.

    Tuni rundunar IRGC ta Iran ta sanar cewa ta kai hari kan wuraren sojojin Amurka, inda ta ce ta nufi sansanin Ali al-Salem da ke Kuwait, da kuma hedikwatar rundunar ruwa ta Amurka da ke Bahrain.

    Rundunar ta ce ta kai waɗannan hare-hare ne da makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa.

  10. Ministan harkokin wajen Iran zai kai ziyara Iraq yau

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, zai kai ziyara ƙasar Iraq a yau Lahadi tare da wata tawaga ta diflomasiyya.

    Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Ismail Baghai, ya ce a yayin ziyarar, za a tattauna dangantakar ƙasashen biyu tare da nazarin halin da ake ciki a yankin da kuma duniya baki ɗaya, a tattaunawa da manyan jami’an gwamnatin Iraq.

    Ya ƙara da cewa ɓangarorin biyu za su yi musayar ra’ayi kan muhimman batutuwa da suka shafi siyasa da tsaro a yankin, da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin Iran da Iraq.

  11. Mun kai hari kan wuraren sojin Amurka guda 8 a Kuwait da Bahrain - Iran

    Rundunar juyin juya halin Iran IRGC ta Iran ta sanar cewa da safiyar Lahadi ta kai hari kan muhimman wuraren sojojin Amurka a ƙasashen Kuwait da Bahrain, ta da makamai masu linzami da kuma jirage marasa matuƙa.

    A wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce ta kai harin ne a wurare takwas na sojojin Amurka, ciki har da sansanin jiragen sama na Ali al-Salem Air Base da ke Kuwait, da kuma hedikwatar rundunar ruwa ta Amurka ta Fifth Fleet da ke Bahrain.

    Rundunar ta IRGC ta ce wannan hari martani ne ga hare-haren da Amurka ta kai a baya.

    Sai dai har yanzu jami'an Amurka ba su yi tsokaci ba kan girman ɓarnar da aka yi ko yiwuwar asarar rayuka.

    Haka kuma IRGC ta zargi Amurka da kai hari kan sansanonin ruwan Iran guda biyar, tana mai cewa an yi hakan ne da sunan cewa rundunar ruwan IRGC ta tare wani jirgi.

    Sanarwar ta jaddada cewa bisa yarjejeniyar da aka cimma, Iran ce ke da alhakin kula da zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar Hormuz, kuma daga yanzu rundunar IRGC za ta ɗauki matakai masu tsauri kan duk wani jirgin ruwa da ta ɗauka a matsayin “mai karya doka.”

  12. Assalamu alaikum

    Masu bibiyarmu a shafinmu na BBC hausa kai tsaye barkanmu da safiyar yau Lahadi.

    Kamar dai yadda aka saba wannan shafi ne da zai kawo muku labarai na abubuwan da ke faruwa a Gabas ta Tsakiya, da Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.