Faransa ta nemi taron gaggawa na MDD bayan Isra'ila ta karɓe gidan tarihi a Lebanon
Ministan harkokin wajen Faransa, Jean-Noël Barrot, ya sanar da cewa Faransa ta nemi a kira taron gaggawa na Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya bayan rahoton kwace tsohon katanga mai tarihi na Beaufort da sojojin Isra’ila suka yi a Lebanon.
Barrot ya bayyana hakan ne a tashar talabijin na BFM, inda ya ce duk da cewa Faransa na amincewa da ‘yancin Isra’ila na kare kanta, babu wani dalili da zai halatta ci gaba da ayyukan soji da fadada shiga cikin yankin Lebanon.
Ya nuna damuwa kan yadda ake kara faɗaɗa kasancewar sojojin Isra’ila a ƙasar Lebanon, yana mai cewa dole ne Majalisar Tsaro ta duba lamarin cikin gaggawa.
A gefe guda, Ministan Tsaron Isra’ila ya sanar cewa an karɓe sansanin tarihi da muhimmanci na Shaqif (Beaufort), inda ya ce sojojinsa sun sake komawa wurin bayan shekaru 44 tun daga yakin Lebanon na 1982, sannan suka daga tutar Isra’ila a wurin.
Wannan katafaren gini mai tarihi yana da mahimmanci a fannin soja saboda yana bai wa mai rike shi damar ganin yawancin kudancin Lebanon, lamarin da ke kara masa muhimmancin dabarun yaki.