Jam’iyyar NDC ta tsayar da Peter Obi a matsayin ɗan takarar shugaban kasa, Kwankwaso mataimakinsa

Asalin hoton, @KwankwasoRM
Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) ƙarƙashin jagorancin Sanata Seriake Dickson ta bayyana tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, a matsayin dan takararta na shugaban kasa a zaben shekarar 2027.
An bayyana Obi a matsayin wanda zai yi wa jam’iyyar takara ne a babban taron jam’iyyar da aka gudanar a Abuja ranar Asabar.
Bayan karbar tutar jam’iyyar, Obi ya sanar da tsohon gwamnan Jihar Kano, Musa Kwankwaso, a matsayin abokin takararsa.
Fitowar Obi a matsayin dan takarar NDC ya sake bude gasar neman shugabancin kasa tsakanin manyan 'yan siyasa uku.
Wannan na zuwa ne bayan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya lashe tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, yayin da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC.
Atiku da Obi dai da farko sun shiga ADC tare da wasu manyan 'yan adawa a watan Yulin 2025 a wani yunƙuri na hada kan adawa domin ƙalubalantar APC a zaben 2027. Sai daga baya Obi ya fice daga ADC tare da Kwankwaso, inda suka koma NDC.
Shigowar Obi da Kwankwaso cikin NDC tare da magoya bayansu na kungiyoyin Obidient Movement da Kwankwasiyya Movement ya ƙara wa jam’iyyar ƙarfi a fagen siyasa.














