Dzeko zai shiga jerin masu shekara 40 da suka buga kofin duniya, Gasar kofin duniya
Tsohon ɗan wasan Manchester City, Edin Džeko na shirin shiga cikin jerin fitattun ƴan kwallo masu shekara 40 ko fiye da haka da suka buga a gasar cin kofin duniya, bayan da aka saka shi cikin tawagar Bosnia and Herzegovina da za ta bana.
Ɗan wasan tawagar Kamaru, Roger Milla ya taka leda kuma ya ci ƙwallo a gasar ta 1994.
Haka kuma akwai masu tsaron raga shida da suka yi hakan — Essam El Hadary na Masar, wanda yake da shekara 45 a gasar cin kofin duniya a 2018, Faryd Mondragón na Colombia da Pat Jennings na Ireland ta Arewacin da Peter Shilton na Ingila da Dino Zoff na Italiya da Ali Boumnijel na Tunisia.
Ana kuma sa ran Luka Modrić mai shekara 40 da Cristiano Ronaldo mai shekara 41 za su taka leda ga ƙasashensu, Croatia da Portugal a gasar ta bana.