Marmoush zai kara yin fice a sauran wasan Man City a kakar nan, Manchester City
Pep Guardiola ya bayyana cewa Omar Marmoush zai taka muhimmiyar rawa a wasannin da suka rage wa Manchester City a kakar nan
City na da sauran wasa huɗu kafin kakar nan ta karkare, ciki har da wasan ƙarshe a FA Cup da Chelsea a Wembley - kenan cikin kwana 12, ƙungiyar za ta yi fatan lashe dukkan wasannin da suka rage mata.
Ɗan wasan tawagar Masar, Marmoush bai samu damar taka leda sosai ba a wannan kakar, inda ya fara da karawa bakwai a Premier League. Sai dai ya nuna ƙwarewarsa lokacin da ya zura ƙwallo a raga a wasan da City ta doke Brentford 3-0, wanda ya shiga canjin ɗan wasa a ranar Asabar.
Guardiola ya ce yana sa ran Marmoush da sauran ƴan wasan da ba sa fara wasa akai-akai, za su kasance cikin shiri idan aka nemi gudummawarsu a koda yaushe.
Marmoush yana sha zama a benci ne saboda kasancewar Erling Haaland, wanda ya ci ƙwallonsa ta 50 a bana yana kan ganiya.

Asalin hoton, Getty Images






