KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Juma'a 15/05/2026

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, da Usman Minjibir da Aisha Babangida

  1. Ukraine ta kai harin jirgi mara matuƙi kan Rasha

    Ukraine ta kai hari da jiragen yaƙi mara matuƙa a birnin Ryazan na ƙasar Rasha.

    Kafofin yaɗa labaran Ukraine sun ce wuraren da aka kai harin sun haɗa da matatar mai, inda gobara ta tashi cikin dare.

    Gwamnan yankin ya ce mutum uku ne aka kashe.

    Harin na Ukraine dai ya biyo bayan harin da jiragen saman Rasha suka kai kan Kyiv a jiya Alhamis, inda aka kashe aƙalla mutum ashirin da ɗaya.

    Wannan dai na daga cikin abin da jami'an Ukraine suka ce shi ne hari mafi girma da suka fuskanta ta sama tun da Rasha ta fara mamayar ƙasarsu.

  2. Mutum 65 sun mutu bayan ɓarkewar cutar Ebola a Congo

    ...

    Asalin hoton, Universal Images Group via Getty Images

    An tabbatar da ɓarkewar cutar Ebola a Lardin Ituri na Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo inda hukumar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa ta Afirka ta ce an samu rahoton mutum 246 da ake zargin sun kamu, wasu 65 kuma sun mutu, galibi a Mongwalu da Rwampara.

    Duka garuruwan sun dogara ne kan zinare a matsayin kafar samun kuɗaɗen shigarsu.

    Gwaje-gwajen da aka yi a Kinshasa su gano mutum 13 cikin 20 ɗauke da ƙwayar cutar sannan kuma ana ci gaba da nazarin waɗanda ake zargin suna ɗauke da cutar.

    Mutane huɗu da suka mutu na cikin waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar.

    Har yanzu gwamnatin ƙasar ba ta ayyana ɓullar cutar a matsayin ɓarkewa ba sai dai ana sa ran hukumomi su yi taron manema labarai nan gaba.

  3. APC ta ɗage zaɓen fitar da gwani na ƴanmajalisar wakilai

    Nentawe Yilwatda

    Asalin hoton, X/Nentawe Yilwatda

    Jam'iyya mai mulki a Najeriya, APC ta ɗage zaɓen fitar da ƴantakara na ƴanmajalisar wakilai da aka tsara yi a yau zuwa gobe Asabar.

    Wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na jam'iyyar, Felix Morka, ya fitar, ta ce sauyin bai shafi zaɓen fitar da gwani da sanatoci da majalisun dokoki na jihohi da na gwamnoni da kuma shugaban ƙasa ba.

    Ya ce a yanzu zaɓen fitar da gwani na sanatoci zai gudana ranar Litinin 18 ga watan Mayu, na ƴanmajalisar jiha kuma za a yi shi a ranar Laraba 20 ga watan Mayu sai na gwamnoni da aka tsara yi ranar Alhamis 21 ga watan Mayu.

    Sanarwar ta ƙara da cewa zaɓen fitar da ɗantakarar shugaban ƙasa a jam'iyyar zai gudana kamar yadda aka tsara wato a ranar 23 ga watan Mayu sai dai Morka bai faɗi dalilin ɗagewar ba.

    Ya ce matakin ya shafi tsarin jigila musamman ga jami'an da aka tsara za su je sa ido a zaɓen.

  4. Trump ya bar China bayan ƙarƙare tattaunawa da Xi Jinping a Beijing

    Shugaba Trump da Xi Jinping

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Donald Trump na Amurka ya bar ƙasar China bayan tattaunawar da ya yi da takwaransa Xi Jinping a Beijing kan yauƙaƙa alaƙa tsakanin ƙasashen masu ƙarfin tattalin arziki.

    Mista Trump ya ce sun ƙulla yarjeniyoyin kasuwanci masu ban sha'awa, kodayake bai bayar da cikakken bayani ba.

    Wakilin BBC ya ce yayin wata ganawa da suka yi a babban ɗakin taron jama'a shugaba Xi ya gargaɗi Donald Trump kan cewa batun Taiwan na iya janyo matsala tsakanin ƙasashen biyu idan har ba a tafiyar da shi yadda ya kamata ba.

    Tun da farko Mista Trump ya shaida wa gidan talabijin na Fox News cewa China ta amince ta sayi mai daga Amurka, za ta kuma daina bai wa Iran kayan aikin soji.

    Kan batun yaƙin na Iran dai, wani kakakin ma'aikatar harkokin wajen China ya shaida wa manema labarai cewa tun farko bai kamata ma a fara yaƙin ba kuma yanzu babu dalilin ci gaba da shi.

  5. Barka da Juma'a

    Shafin Kai Tsaye na BBC Hausa na yi wa ɗumbin masu kasancewa da mu barka da wannan lokaci.

    Da fatan an wayi gari cikin ƙoshin lafiya. Kamar kodayaushe, a yau ma za mu ci gaba da kawo maku rahotanni na abubuwan da suka shafi yaƙin Iran da labaran da suka danganci Najeriya da sauran ƙasashen duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labarai da ma kallon bidiyo.