KAI TSAYE, Yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai kan abubuwan da ke faruwa tsakanin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma sauran muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 08/06/2026.

Skip Bidiyo and continue reading
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Sadis Buba
  • Pantami
  • xxx
  • Nafiu Gombe
  • Mace da ƴarta mai lalaurar Autism
  • wata mata
  • BBC reporter

Rahoto kai-tsaye

Muslim Muhammad Yusuf, Aisha Babangida da Usman MINJIBIR

  1. Amurka ce ke da alhakin hare-haren Isra’ila a ƙasarmu - Iran

    ....

    Asalin hoton, Tasnim news agency

    Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Ismail Baqaei, ya ce Amurka ce ke da alhakin hare-haren da Isra’ila ta kai wa Iran.

    Da yake magana a taron manema labarai na mako-mako, Baqaei ya bayyana cewa duk wani abu da ya faru a yankin, to Amurka ce za ta ɗauki alhakin hakan.

    “Duk abin da ya faru a yankin, ko Amurka da kanta ce ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta ta hanyar kai hare-hare kan jiragen kasuwancin Iran da kutsawa yankunan kudancin kasar da dai sauransu, Amurka ce ke da alhaki kai tsaye.

    Haka kuma sakamakon duk wani ƙarin tashin hankali zai rataya a wuyanta.”

    Bayan hare-haren da Isra’ila ta kai a daren jiya, jami’an Amurka sun bayyana cewa sojojin Amurka ba su da hannu a harin.

    Sai dai Baqaei ya ce rundunar sojojin Amurka ta CENTCOM tana aiki tare da Isra’ila a ɓangarorin kai hari da kuma kariya.

    Da aka tambaye shi game da rahotannin da ke cewa an kai hari sansanin sojin Yarima Sultan da ke Saudiyya, Baqaei ya ce rundunar sojin Iran kan sanar a hukumance duk wurin da ta kai hari.

  2. Iran ta kai harin ramuwar gayya kan cibiyoyin man Isra'ila

    Iran

    Asalin hoton, Getty Images

    Dakarun juyin juya halin Iran, IRGC, sun ce sun ƙaddamar da hare-haren ramuwar gayya da makamai masu linzami kan cibiyoyin man Isra'ila da ke Haifa.

    A wata sanarwa da IRGC ta fitar, ta ce ta kai harin ne bayan da Isra'ila ta kai mata hari kan cibiyoyin man ƙasarta.

    Isra'ila ta kai harin ne kan matatar man Iran ta Karun Mahshahr. duk da yake IRGC ba ta bayyana sunan matatar a bayanin nata ba.

    Ta ƙara da cewa, "kai hare-hare kan fararen hula da matatun mai babbar barazana ce da za ta iya jefa yankin cikin matsalar makamashi",

    Kakakin hukumar kula da cibiyoyin man ya bayyana a wata sanarwa cewa: "an kai hari sau biyu a kan matatar ta Karun" amma ba a samu jikkatar mutane ba kuma ana ci gaba da duba ɓarnar da harin ya yi.

  3. Iran ta dakatar da zirga-zirgar jiragen sama

    Iran

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran ta dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a babban filin jiragen sama na ƙasa da ƙasa da ke babban birnin ƙasar, Tehran.

    Haka kuma an rufe sararin samaniyar yammacin ƙasar har sai abun da hali ya yi.

    A Syria ma mahukunta sun dakatar da sauka da tashin jiragen sama a babban birnin kasar Damascus, tare da rufe sararin samaniyar kudancin ƙasar na tsawon sa’o’i goma sha biyu.

    Ita ma Iraqi ta sanar da rufe sararin samaniyarta na tsawon sa’o’i saba’in da biyu.

  4. Iran da Isra’ila sun yi wa juna ruwan wuta da makamai masu linzami

    Iran da Isra'ila sun kai hari

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran da Isra’ila sun ci gaba da musayar hare-haren makamai masu linzami cikin dare har zuwa safiyar yau Litinin.

    Wannan na zuwa ne bayan harin da Iran ta kai arewacin Isra’ila a ranar Lahadi, wanda shi ne na farko tun bayan tsagaita wuta da aka cimma a watan Afrilu.

    Tehran ta ce harin da ta kai shi ne na farko, a jerin hare-haren da za ta shafe mako guda tana kai wa Isra'ila, wadda ta zarga da keta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma ta hanyar kai hari Lebanon.

    Zuwa yanzu ba a bayar da rahoton samun asarar rayuka sakamakon hare-haren ba.

    Isra'ila ta mayar da martani duk da cewa Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bukaci kada ta ta tanka Iran, saboda hakan na iya mayar da hannun agogo baya.

    Yanzu haka rahotanni na cewa dakarun tsaron Isra'ilar sun bada wata sabuwar sanarwar gargadi ga jama'a da ke cewa Iran din ta sake harbo karin wasu makamai masu linzami, don haka jama'a su yi maza su shige wuraren neman mafaka da aka tanada.

    Bayanai na cewa ita ma kungiyar Huthi da ke Yemen da Iran din ke mara wa baya ta harba wa kasar makami mai linzami wanda yanzu haka ke kan hanya.

  5. Barka da safiya!

    Barka da zuwa shafin BBC Hausa na kai-tsaye wanda ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa game da yaƙin Iran da kuma muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a wannan rana ta Litinin,

    Za ku iya yin tsokaci a shafukanmu na sada zumunta: Facebook, X, instagram, YouTube da kuma zaurenmu na WhatssApp.