An umarci jami’an ƴansanda su ɗauki mataki kan masu riƙe da makamai ba bisa ƙa’ida ba

Asalin hoton, @PoliceNG
Sufeto Janar na ƴanSandan Najeriya, Olatunji Disu, ya umarci jami’an ‘yan sanda a faɗin ƙasar su ɗauki mataki mai tsauri kan duk wanda aka samu da makamai ba bisa ƙa’ida ba.
Ya ce jami’an su yi amfani da tanadin dokar aiki ta Force Order 327 wajen tunkarar masu laifi domin daƙile hare-hare da kuma dawo da zaman lafiya musamman a Jihar Benue.
Disu ya bayar da umarnin ne a wani taron tattaunawa da ya yi da Gwamnan Jihar Benue, Hyacinth Alia, a Makurdi, yayin wata ziyarar aiki da ya kai jihar sakamakon yawaitar kashe-kashe da hare-haren da ake fuskanta.
Mahalarta taron sun bayyana damuwa kan hare-haren da ake kai wa tare da tambayar dalilin da ya sa wasu barazanar tsaro ke ci gaba duk da bayanan sirri da ake bai wa hukumomi.
Sufeto Janar ɗin ya kuma buƙaci matasan jihar Benue su ƙara haɗa kai da ‘yansanda wajen tattara bayanan sirri da za su taimaka wajen yaƙi da laifuka.
A nasa ɓangaren, Gwamna Alia ya sake kira da a kafa ‘yan sandan jihohi domin taimakawa wajen magance matsalar tsaro.


















