Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 7/08/2026

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Juma'a 7 ga watan Agustan 2026.

Rahoto kai-tsaye

Daga Muslim Muhammad Yusuf

  1. Somalia ta yi maraba da yarjejeniyar tsaron Sadiyya, Turkiyya da Pakistan

    Gwamnatin Somalia ta fitar da sanarwa kan yarjejeniyar tsaron bai ɗaya da aka sanya wa hannu a yau tsakanin Saudiyya, Turkiyya da Pakistan.

    Yarjejeniyar ta tanadi cewa duk wani hari da aka kai wa ɗaya daga cikin ƙasashen uku za a ɗauke shi a matsayin hari da aka kai wa dukkansu.

    A cikin sanarwar da Ma'aikatar Tsaron Somalia ta fitar, ta taya ƙasashen Musulmi murnar rattaba hannu kan yarjejeniyar.

    Sanarwar ta ce: "Ma'aikatar Tsaron Jamhuriyar Tarayyar Somalia na taya Masarautar Saudiyya, Jamhuriyar Turkiyya da Jamhuriyar Musulunci ta Pakistan murnar sanya hannu kan Yarjejeniyar Makka ta Tsaron Bai Ɗaya."

    Somalia ta bayyana yarjejeniyar a matsayin wani muhimmin mataki na tarihi wajen ƙarfafa tsaro na bai ɗaya, bunƙasa haɗin gwiwar tsaro da kuma gina ingantaccen kawance da dabarun tsaro domin tunkarar barazanar tsaro da ƙasashen ke fuskanta tare.

    Ma'aikatar Tsaron ta kuma bayyana cewa wannan yarjejeniya za ta taimaka wajen ƙarfafa ƙoƙarin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin da ma duniya baki ɗaya, tare da inganta ƙa'idojin haɗin gwiwa, haɗin kai da ɗaukar nauyi tare.

    Ta ƙara da cewa yarjejeniyar za ta amfani al'ummomin yankin, tare da tallafa wa ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya da ingantaccen tsaro.

  2. Saudiyya da Turkiyya da Pakistan sun sa hannu kan yarjejeniyar tsaro

    Turkiyya ta jaddada cewa yarjejeniyar tsaro haɗaka da ta sanya hannu tare da Saudiyya da Pakistan a yayin da ake ci gaba da rikici tsakanin Amurka da Iran ba a yi ta domin ƙalubalantar wata kasar takamaimai ba.

    Daraktan Hukumar Sadarwa ta Fadar Shugaban Turkiyya, Burhanuddin Duran, ya rubuta a shafinsa na X cewa: "Yarjejeniyar da aka cimma a Makka ba ta da niyyar kalubalantar wata ƙasa ta musamman. Za ta ƙarfafa tsaron bai ɗaya da ƙarfin daƙile barazana na ƙasashen uku, kuma ta wannan hanya za ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankinmu."

    A baya Saudiyya ma ta bayyana irin wannan matsayi.

    Sai dai, kamar yadda aka ruwaito a baya, sanya hannu kan wannan yarjejeniya ya haifar da martani mai ƙarfi daga Iran, musamman daga Ibrahim Rezaei, memba a Kwamitin Tsaro na Ƙasa da Harkokin Waje na Majalisar Ƙoli Musulunci ta Iran.

    Mista Rezaei ya rubuta a shafinsa na X cewa: "Ya kamata ‘yan Saudiyya su sani cewa yarjejeniya a takarda kawai da Turkiyya da Pakistan ba za ta kawo musu tsaro ba, kamar yadda shekarun da aka kwashe na dogaro da Amurka don samun kariya ba su kawo musu tsaro ba."

  3. DSS ta gurfanar da tsohon jami'inta bisa zargin alaƙa da IPOB

    Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Najeriya (DSS) ta gurfanar da wani tsohon jami'inta, Nwaogu Ihechimere Ezeakolam, a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja bisa zargin kasancewa mamba a haramtacciyar ƙungiyar IPOB.

    An gurfanar da shi ne ranar Alhamis a gaban Mai Shari'a Mohammed Garba Umar kan tuhume-tuhume guda huɗu da gwamnatin tarayya ta shigar.

    DSS na zargin Ezeakolam da bai wa IPOB goyon baya da kayan aiki, shiga ƙungiyar duk da sanin cewa an haramta ta, da kuma wallafa saƙonni a shafukan sada zumunta domin ƙarfafa jama'a su mara mata baya, wanda ta ce ya saɓa wa tanade-tanaden dokar yaƙi da ta'addanci ta shekarar 2022.

    Sai dai bayan an karanta masa tuhume-tuhumen, tsohon jami'in ya musanta aikata dukkan laifukan.

    Mai shari'a ya ɗage shari'ar zuwa 29 ga Oktoba domin fara sauraron ta, sannan ya ba da umarnin a ci gaba da tsare shi a gidan gyaran hali na Kuje har sai an yanke hukunci kan buƙatar belinsa.

    A shekarar 2017, gwamnatin Najeriya ta ayyana IPOB a matsayin ƙungiyar ta'addanci tare da haramta ayyukanta.

  4. Isra'ila ta kori manyan jami'an Mossad biyu saboda sun kasa kifar da gwamnatin Iran

    Kafofin yaɗa labaran Isra'ila sun ce shugaban hukumar leƙen asiri ta Mossad, Roman Goffman, ya sallami manyan jami'ai biyu na hukumar bisa zargin cewa su ne suka tsara shirin da bai yi nasarar kifar da gwamnatin Iran ba.

    Tashar talabijin ta Channel 12 ta Isra'ila ta ruwaito cewa ɗaya daga cikin jami'an da aka kora ya jagoranci sashen tattara bayanan sirri na Mossad tun watan Disamban 2015, yayin da ɗayan kuma yake shugabantar sashen da ke kula da harkokin Iran. Sai dai ba a bayyana sunayensu ba.

    Rahoton ya ce jami'an biyu ne suka tsara wani shirin aiki na sirri da nufin kifar da Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta hanyar amfani da ƙungiyoyin Kurdawa da kuma tayar da zanga-zangar gama-gari a ƙasar.

    Rahotannin sun ƙara da cewa Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya gabatar da wannan shiri ga Shugaban Amurka, Donald Trump, a lokacin da yake ƙoƙarin shawo kansa ya kai hari kan Iran a watan Maris.

    A lokacin da aka tsara shirin, David Barnea ne ke jagorantar Mossad, kafin daga bisani Roman Goffman ya maye gurbinsa a watan Yunin wannan shekara.

  5. Dole al'umma su taka rawa wajen daƙile yaɗuwar Ebola - CDC

    Cibiyar Yaƙi da Cututtuka ta Afirka (CDC) ta ce dole ne al'ummomi su taka muhimmiyar rawa wajen shawo kan annobar Ebola da ke ci gaba da yaɗuwa a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kwango (DRC).

    Shugaban cibiyar, Dr Jean Kaseya, ya shaida wa BBC cewa sanya shugabannin al'umma cikin yaƙi da cutar zai taimaka wajen yaƙi da yaɗa bayanan ƙarya, gano masu ɗauke da cutar da wuri, da kuma ƙarfafa bin hanyoyin binne gawa cikin aminci.

    Ya ce ana kuma shirin matsa wa da cibiyoyin gwajin Ebola da sauran ayyukan kiwon lafiya kusa da al'ummomi domin sauƙaƙa samun kulawa.

    Kalaman nasa na zuwa ne yayin da adadin waɗanda aka tabbatar sun kamu da Ebola a DRC ya haura 4,000, kuma cutar ta yi sanadin mutuwar kusan mutum 1,800.

  6. Saudiya, Turkiyya da Pakistan sun ƙulla yarjejeniyar tsaro

    Saudiya, Turkiyya da Pakistan sun rattaba hannu kan wata yarjejeniyar tsaro domin ƙarfafa haɗin gwiwarsu a fannin tsaro.

    An sanya hannu kan yarjejeniyar ne a birnin Makka, inda Yarima mai jiran gado na Saudiya, Mohammed bin Salman, da Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, da Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif, suka halarta.

    Bisa yarjejeniyar, duk wani hari da aka kai kan ɗaya daga cikin ƙasashen uku za a ɗauke shi a matsayin hari kan dukkaninsu.

    Wannan haɗin gwiwar na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da yaƙi tsakanin Amurka da Iran, rikicin da ya shafi wasu ƙasashen yankin Tekun Fasha tare da kawo cikas ga zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigar Hormuz da kuma Tekun Maliya.

  7. Ƴan sanda sun ƙwato dabbobi sama da 450 daga hannun ƴanbindiga a Sokoto

    Rundunar Ƴan Sandan Jihar Sokoto ta ce ta yi nasarar daƙile hare-haren ƴanbindiga guda biyu a ƙananan hukumomin Shagari da Rabah, inda ta ƙwato dabbobi sama da 450 da maharan suka kwashe.

    A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Ahmad Rufa'i, ya fitar, ya ce harin na farko ya faru ne da misalin ƙarfe 7:20 da yammacin ranar 4 ga Agusta, lokacin da ƴanbindiga ɗauke da makamai suka kai hari ƙauyukan Horo Birni da Marake a ƙaramar hukumar Shagari.

    Sanarwar ta ce bayan samun kiran gaggawa, jami'an rundunar da sojoji suka iza zuwa wurin, inda suka yi musayar wuta da maharan.

    Ya ce maharan sun tsere zuwa cikin daji bayan sun sha ƙarfinsu, tare da barin dabbobin da suka kwashe, waɗanda suka haɗa da shanu 195, tumaki 84 da raƙuma biyu.

    Sai dai mutum biyu daga cikin mazauna yankin sun samu raunukan harbin bindiga, kuma an kai su asibiti domin samun kulawa.

    A wani hari daban da ya faru da misalin ƙarfe 8:10 na dare a ƙauyen Maikujera da ke ƙaramar hukumar Rabah, ƴanbindiga sun sace dabbobi 171, da suka haɗa da raƙuma, shanu, tumaki da awaki.

    Rundunar ta ce jami'anta sun tare hanyoyin fita daga ƙauyen tare da fafatawa da maharan, lamarin da ya tilasta musu tserewa tare da barin dukkan dabbobin da suka sace.

  8. Mayaƙan Houthi sun kashe dakarun gwamnatin Yemen 58

    Mayaƙan Houthi na Yemen sun kashe aƙalla dakarun gwamnatin Yemen 58 a hare-haren makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa da suka kai ranar Alhamis.

    Wata majiyar soji ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa wannan na daga cikin hare-haren da suka fi muni tun bayan ɓarkewar yaƙin Yemen kusan shekara huɗu da suka gabata.

    Hare-haren na zuwa ne yayin da mayaƙan Houthi suke ƙara kai hare-hare kan dakarun gwamnatin Yemen da kuma Saudiya.

    Mai magana da yawun sojojin Houthi, Yahya Saree, ya ce ƙungiyar ta kai hare-haren ne da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa a matsayin martani ga abin da ya kira shirin soja da Saudiya ke marawa baya.

    Wata majiya ta soja da ta nemi a sakaya sunanta ta ce sama da dakaru 58 ne suka mutu, yayin da wasu da dama suka jikkata.

    Ma'aikatar Tsaron Yemen ta ce dakarunta za su mayar da martani kan hare-haren "a lokacin da ya dace da kuma wurin da ya dace."

  9. Buga fasfo ne aka mayar Abuja, ba karɓarsa ba - Immigration

    Hukumar Kula da Shige da Fice ta Najeriya (Immigration) ta ce sabon tsarin da ta bullo da shi na mayar da buga fasfo a Abuja bai shafi karɓa ko yin rijistar fasfo a jihohi ba.

    Hukumar ta ce rahotannin da ke cewa za a ɗauke cibiyoyin gudanar da fasfo daga Kano ba gaskiya ba ne, kuma mutane sun yi kuskuren fahimtar abin da ake nufi.

    Bayanin na zuwa ne yayin da ake ci gaba da cece-ku-ce kan wata takarda da ta nuna cewa an mayar da wasu cibiyoyin buga fasfo daga wasu jihohin zuwa Abuja kaɗai.

    Jami'in hulɗa da jama'a na hukumar a jihar Kano, DSI Muhammad Auwal, ya shaida wa BBC cewa sabon tsarin ya fara aiki tun farkon shekarar nan, kuma an aiwatar da shi a wasu jihohin a rukuni-rukuni.

    "Ba wai za a daina rijistar fasfo ko kuma karɓarsa a jihohi ba ne. Buga fasfo ne aka mayar zuwa Abuja," in ji shi.

    Ya ƙara da cewa, an fara aiwatar da tsarin ne a jihohin Nasarawa, Kogi, Borno da Yobe, kuma za a ci gaba da faɗaɗa shi zuwa sauran jihohi.

    DSI Auwal ya tabbatar wa BBC cewa takardar da ake ta yaɗawa daga hukumar ta fito, amma ya ce takarda ce ta cikin gida wadda ba a yi niyyar ta fito bainar jama'a ba.

    Ya ce manufar mayar da buga fasfo wuri guda ita ce ƙarfafa tsarin tsaro da kuma rage yiwuwar buga fasfo na bogi.

    Dangane da rashin ganin Legas cikin jerin jihohin da sauyin ya shafa, ya ce "ita ma tana cikin rukuni na biyar," kuma za a aiwatar da sabon tsarin a can nan ba da jimawa ba.

  10. Ɗalibi ya kashe mutum shida da bindiga a makaranta a Thailand

    'Yan sanda a Thailand sun ce wani ɗalibi mai shekara 14 ya buɗe wuta a wata makaranta da ke Nonthaburi, kusa da Bangkok, inda ya kashe mutum shida, ciki har da ɗalibai da malamai.

    Aƙalla mutum 15 kuma sun jikkata a harin.

    'Yan sanda sun ce sun fara bincike kan abin da ya sa ɗalibin ya aikata harin.

    Hotunan da aka yaɗa sun nuna yadda ɗalibai suka riƙa gudu cikin firgici suna ihu bayan harbin, yayin da motocin agajin gaggawa suka isa makarantar domin kai ɗauki.

  11. Gwamnati da ƴan adawa a Venezuela sun fara tattaunawar miƙa mulki

    Wakilan gwamnatin riƙon ƙwarya da na ƴan adawa a Venezuela sun kammala zama na farko na tattaunawa kan yadda za a gudanar da miƙa mulki cikin lumana.

    Bangarorin biyu sun amince da yin aiki tare domin samar da mafita da za ta yi daidai da kundin tsarin mulkin ƙasar.

    Amurka na goyon bayan wannan tattaunawa bayan sauyin mulkin da ya kawo ƙarshen shugabancin Nicolas Maduro a watan Janairu.

    Amurka na da tasiri mai ƙarfi kan gwamnatin riƙon ƙwarya ta Venezuela, kuma tana matsa mata lamba domin a bai wa kamfanoninta damar zuba jari a fannin haƙo mai da sauran ma'adanan ƙasar.

  12. 'Harin Houthi kan iyakar Saudiya ya jikkata mutum 11'

    Gwamnatin Yemen da ke samun goyon bayan Saudiya, kuma wadda ƙasashen duniya suka amince da ita, ta ce mutum 11 sun jikkata sakamakon harin da mayaƙan Houthi suka kai a yankin Najran, da ke kusa da kan iyakar Saudiya.

    Harin ya zo ne kwana biyu bayan da ƴan Houthi masu samun goyon bayan Iran suka sanar da cewa sun kai hari da jirgin sama marar matuƙi kan filin jirgin saman Najran.

    Lamarin na ƙara nuna tsanantar rikicin ne, bayan da ƴan Houthi suka ayyana cewa sun toshe zirga-zirgar jiragen ruwa a Tekun Maliya, tare da kai hare-hare kan jiragen dakon man Saudiya cikin makonni biyun da suka gabata.

  13. Kotu ta ci kamfanin Meta tarar $567m kan gaza kare lafiyar yara

    Wata kotu a Amurka ta ci kamfanin Meta tarar dala miliyan 567 saboda gazawarsa wajen kare lafiyar yara masu amfani da shafukan Facebook da Instagram.

    Rahotanni sun ce wannan ita ce mafi girman tarar da aka taɓa cin kamfanin.

    Alƙalin da ya yanke hukuncin ya ce Meta ya taka rawa wajen ƙara matsalolin lafiyar ƙwaƙwalwa da damuwar da wasu matasa ke fuskanta sakamakon amfani da shafukan sada zumunta.

    Kotun ta kuma umarci kamfanin da ya sauya yadda matasa ke amfani da shafukansa, bayan gano cewa tsarin da yake amfani da shi na iya yin illa ga lafiyar ƙwaƙwalwarsu.

    Sai dai Meta ya ce yana da tsauraran ƙa'idoji da matakan kare yara a dandalinsa, tare da sanar da cewa zai ɗaukaka ƙara kan hukuncin.

  14. Jumu'atu Babbar Rana!

    Jama'a Mubarak masu bibiyar wannan shafi na kai tsaye daga BBC Hausa.

    A wannan shafi za mu ci gaba da kawo muku labaran abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Muslim Muhammad Yusuf tare da sauran abokan aiki za mu kasance da ku.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na Facebook da X da kuma Whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.